Zaman Tare (i)

0
1833

1.Bismillahi mai rahma,

Salatin ka ga mai girma,

Muhammadu Ɗaha ja rahama,

A duniya har Ƙiyama ma,

Mai son mu yi zamantare.

 

  1. Shimfiɗa ɗaya za mu zauna

Ni da kai zo nan mu zauna

In da ke zo nan mu zauna

In da ku ma zo mu zauna

Tabarmar ta mu ce tare.

 

  1. Ɗaki ɗaya ne fa namu

Ga gadaje nan fa namu

Shimfiɗu ne muka samu

Babu komi kar mu damu

Sai mu kwana abin mu tare.

 

  1. Kar ka hau mini kai in hauka

Ba ka Ƙi na ba ni Ƙinka

In gida na ɗaya da naka

Ga shiyya na ga shiyyarka

Sai mu gyara gidanmu tare.

 

  1. Mun haɗe kuma unguwarmu

Ga gida na ko gidanmu

Ga gidan wasu naku namu

Ga iyakokin gidanmu

Duk da naku muna fa tare.

 

  1. Rugga na ɗaya da naka

Ga bukka na da naka

Inda shanu na da naka

Ga iyali na da naka

Mu yi zama mai kyau fa tare.

 

  1. Ƙauye na ɗaya da naka

Karkara na ɗaya da naka

Ko gari na ɗaya da naka

Kai ka sanni ko na sanka

Sai mu so junanmu tare.

 

  1. Mazaɓa, Ƙaramar hukuma

Ko jaha ɗaya muka sama

Ko Ƙasa sai mu yi ta himma

Ci gabanmu da nata har ma

Masu son mu muna fa tare.

 

  1. In uwa ɗaya muka samu

In uba ɗaya muka samu

Mallami ɗaya muka samu

Shugaba ɗaya muka samu

Ba na biyu a gare su tare.

 

  1. Kowanensu mu girmama shi

Kar mu yarda a banzata shi

Yadda duk Allah Ya yi shi

Inda samu ko rashin shi

Inda shi ko ba a tare.

 

  1. In addini guda ne

Haka in yare guda ne

Ko jam’iyya guda ne

Yanki sana’a guda ne

Ko ba haka ga mu tare.

 

  1. Kasuwa ɗaya ce fa tamu

Ko wurin aikin ga namu

Asibiti gun maganinmu

Haka na rafin ga namu

Rijiya ce tamu tare.

 

  1. Kowane Allah ya ba mu

Za mu amfana dukkanmu

Shi ya ba mu Ya ko haɗa mu

Mu kula su da kyau dukkanmu

Namu ne an ba mu tare.

 

  1. Mata da miji kowa da nashi

‘Ya’ya kuma kowa da nashi

Sutura kowa da nashi

Samu kowa da nashi

Duniya kuma ga mu tare.

 

  1. Addini kowa da nashi

Yare kowa da nashi

Hali kowa da nashi

Ƙira kowa da nashi

Allah ya haɗa mu tare.

 

  1. Duk abin da Ya haɗa mu

Ya fi abin da zai raba mu

Haka nan kuma me gina mu

Ya fi me rusa gininmu

Wanda be son ga mu tare.

 

  1. Makaranta ce fa tamu

Sannan ga Mallamanmu

Komi ke ciki an fa ba mu

Babu bambanci ajinmu

HaƘuri za mu yi fa tare.

 

  1. Allah ɗaya ne Ya yi mu

Allah ɗaya ne Ya sanmu

Allah ɗaya ne Ya ba mu

Allah ɗaya ke haɗa mu

Koda mun so mu ware.

 

  1. Allah ɗaya ke rabawa

Shi ne kuma ke haɗau

Shi ne me komi da kowa

Shi ne me baiwa bawa

Addini da wuri da yare.

 

  1. Komi Allah Ya zaɓa

Shi ne bawa ya zaɓa

Hanya mai kyau ka zaɓa

In mummuna ka zaɓa

Sai Ya so ka gane ku tare.

 

  1. Duk abin da ya ba ku tare

Ku haɗe a cikinsa tare

Inda Annabi ga ku tare

Inda shaiɗan ga ku tare

Inda yatsu in kutare.

 

  1. In makahi in guragu

Masu ji bebe da shegu

Ko ka yarda ko ka tsargu

Ga na kirki ga miyagu

Ya haɗa ku, ku ci shi tare.

 

  1. Lafiya ita za ka nema

Da zama a cikinta nema

Kar ka yarda da masu ce ma

Ka ji tsoro don ka koma

Gun tsiya ko sare-sare.

 

  1. Kar ka je inda za a jima

In ka ɗauki fansa a ɗau ma

Kiyayi iyaye, ‘yan uwa ma

Da nashi da naka yana isar ma

Addu’a mai kyawu dai tsare.

 

  1. Allahu ke haɗawa a wuri ɗaya

Waɗansu ya haɗa su a duniya ɗaya

Waɗansu ya haɗa su cikin Ƙasa ɗaya

Waɗansu ya haɗa su a ɓangare ɗaya

Waɗansu ya haɗa su, su yi zamansu tare.

 

  1. Waɗansu ya haɗa su a tare ɗaya

Waɗansu ya haɗa su ba su gu ɗaya

Waɗansu ya haɗa su sana’a ɗaya

Waɗansu ya haɗa su da bauta ɗaya

Waɗansu ya haɗa su daban-daban a tare.

 

  1. Waɗansu ya haɗa su zamansu lafiya

Waɗansu an haɗa su suna ta yin tsiya

Waɗansu an raba su sun sami lafiya

Waɗansu an raba su suna hayaniya

Waɗanda ke da haƘuri suna zamansu tare.

 

  1. Ki ce da ni ban amince da ke ba

Ashe be fi in ce ke ɓarauniya ba

Ka ce ban amince da kayanka ba

Ashe be fi in ce ka cuce ni ba

Duka suna gudana a kan zamanmu tare.

 

  1. Cewa ban amince ma da ɗaki ba

Ashe be fi in ce kai ka ɗauka ba

Ka ce ban amince ma rumfarmu ba

Ashe be fi in ce kai ka ɗiba ba

Ba ka jin ana wannan sai zamana tare.

 

  1. Azzalumi yake sa mutum yin fushi

Ya taso masa in ya cutar da shi

Kana kwance ka bar tashi da shi

In tsaye ne zauna ko ka kwanta da shi

Sababbin haka ai sai zaman tare.

 

  1. Me ramuwa ya Ƙara azzalumi

Wanda ko ya rama daidai hakimi

Wanda ko ya yafe babban malami

Wanda duk ya ɓoye shaida azzalumi

In ana zaman tare a daina tsumbure.

Mu Kwana Nan

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here