Ɗan Arewa Musulmi Da Wanda Ma Ba Musulmi Ba: Mu Nemi Ilimi

0
9682

Da sunanKa Allah

1. Na kira Ka Allah

Da ikonKa Allah

Taimake ni Allah

In kira ga kowa.

 

  1. Ina yabon Rasulu

Muhammadu Halilu

Habibu ne Jalilu

A kan dukkan Rasulu

Ka fi bashi baiwa.

 

  1. Yadda gare ka Rabbu

Ga Ali har Sahabu

Sa Rahmar ka Rabbu

Ga Tabi’an Sahabu

Da Tabi’ut Tabi’awa.

 

  1. Ina kira Musulmi

Da wanda ba Musulmi

Kar mu yi sake da ilimi

Domin sai da ilimi

Ake batun Arewa.

 

  1. Nijeirya ga tamu

Idan fa babu ilimi

Sunanta ba ta samu

In mun sake da ilimi

Sunan yana ɓacewa.

 

  1. Ni na kira ka ɗanta

Nijeriya uwa ta

In har ka amsa ɗanta

Ko ke ki amsa ‘yarta

Ɗan Kudu ko Arewa.

 

  1. Duniya in ka duba

Ɗa kake ko uba

Adamu ne uba

Yarensa ka sa gaba

Da ilimomin Annabawa.

 

  1. Yare duka nashi ne

Addinai nashi ne

Yanku duka nashi ne

Maza, mata nashi ne

Uba ɗaya muke har uwa.

 

  1. Hauwa’u matarsa ne

‘Ya’ya duka nasu ne

Addini nasu ne

Duniya duka nasu ne

Sai mu rungumi ‘yan uwa.

 

  1. Saƙon Allah gare mu

Manzo zai zo gare mu

Allah in zai kira mu

ManzonSa zai kira mu

‘Yan Adamu da Hauwa.

 

  1. Bambanci na Jalla

Haka nan ma ƙabila

Domin mu san shi Jalla

Mu san juna jimilla

Sarakai da talakawa.

 

  1. Bai yi sai don a bi shi

Bai yi ba don a ƙi shi

Bauta a mayar gare shi

Ya so kuma wani ya ƙi shi

Falala adalci ga kowa.

 

  1. Bai wani don ka ƙi shi

Sai in shi ya ƙi shi

Bai wani don ka so shi

Sai in shi ya so shi

Shi kuma ke da kowa.

 

  1. Ɗa na bin uban shi

Uba na bi ga ɗan shi

Mata ga miji ta bi shi

Ya yi wata ba ta bin shi

Ya yi komi da kowa.

 

  1. Wa da ƙani musali

Mai ilimi da jahili

Ka ga abu ba dalili

Sai sababi da ƙanli

Ba yadda bai iyawa.

 

  1. Don haka kama kanka

Bari ta batun wanin ka

Idan ka kama kanka

To, zai kwaikwaye ka

Ya bi ka da taimakawa.

 

  1. Mai hidima ga kansa

Ya taimaki ɗan uwansa

Allah mai taimakonsa

Ya taimaki ɗan uwansa

Shi da yake taimakawa.

 

  1. Kyaun ɗa ƙarami uwarsa

Yana ɗakin uwarsa

Ya zo ɗakin ubansa

Ya gane shiyar ubansa

Kafin na ƙani da wa.

 

  1. Shiya na ƙanin uba

Ko shiya na wan uba

Haka nan na uban uba

Duka ba su kamar uba

Bale fa gidan uwa.

 

  1. Dage da biɗan sani

Zaman banza ba sani

Aikin banza ba sani

Kada ku zauna ba sani

Kuna kallon ‘yan uwa.

 

  1. Mata kai mata cefane

Gida kai masu cefane

Gari kai masu cefane

Ƙasa kai masu cefane

Yanzu ka zama ɗan uwa.

 

  1. Ka ce a yi maka

Can da an maka

Har yanzu ana maka

Sutura har abincinka

Har da ilimi ɗan uwa.

 

  1. Tambayi masu yi maka

Ko kake so ya yi maka

Ka ce wa ke maka

In ko ya amsa maka

Sai ka ƙara tunanuwa.

 

  1. Sayarwa ba ta kamar saye

Mai sayarwa ga mai saye

Kasuwar birni da ƙauye

In babu ilimi ga mai saye

Wa ke da riba mai sayarwa.

 

  1. Mai sayarwa bai da ilimi

Mai saye in yana da ilimi

Shi kan ci riba da ilimi

Komi za ka yi nemi ilimi

In saye ne in sayarwa.

 

  1. Ƙwadago ne za a ba ka

Ko a amsa nan gare ka

In ma sana’a gare ka

Koyo koyarwa da ɗanka

Sai da ilimi ɗan Arewa.

 

  1. Matuƙin jirgi da mota

Babu cutarwa da sata

Mai niƙan injin da Dokta

Maigini da rufi da fenta

Sai da ilimi ɗan Arewa.

 

  1. Kada ka ce ka sami hanya

Ci da sha sutura a duniya

Gida da abin tabiya a hanya

Safe maraice ka kama hanya

Biɗan ilimi maza ɗan Arewa.

 

  1. Biɗan ilimi na ƙara buɗi

Ya hana ka ya sa ka ka gane ruɗi

Ka wadatu da shi ko babu kuɗi

Da ilimi mai mulki kan yi harɗi

Ya miƙe ƙafarsa ya tsere kowa.

 

  1. Ilimi ke sa a yi karatu

Za ka ga me shi na rubutu.

Bai barin nemansa yana karatu

Ko da an taru gabansa ana karatu

Bai barin ɗaukar ilimi ga kowa.

 

  1. Me zai sa kai mai sana’a

Ko mai aiki don jama’a

Da me ƙaramin ilimi ƙana’a

Ka fasa biɗan ilimi da ɗa’a

Kana son ace maka ka fi kowa.

 

  1. Daga kullum kada ka fasa

Neman ilimi kada ka ƙosa

Don addini ko kuma ƙasa

Jahilci maƙiyi na nisa

Har kusa shi ne fiye da kowa.

 

  1. Ba maƙiyi da ya kai kamarsa

Ko shaiɗani ba ya kai sa

Bale maƙiyanka kusa da nesa

Shi ya sa shaɗan ya hana ka yinsa

Yi karatu Allah ke ta cewa.

 

  1. Mafifici Manzonmu Yasin

Ya ce biɗan ilimi ka je Sin

Kafirci nisa suna Sin

Ɗan Saudiyya ya je nema zuwa Sin

Don zaman duniya ga kowa.

 

Mu Kwana Nan

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here