Dan majalisar Dattawa Ya Dauki Nauyin Karatun Mata 10

0
2159

Rabo Haladu Daga kaduna

Danmajalisar dattawa mai  wakiltar mazabar shiyya ta daya a jihar kaduna sanata Sule Usman Hunkuyi,ya baiwa dalibai mata goma gurbin karo karatun aikin likita a jami\’ar musulunci da ke kasar Yuganda.
Sanata Hunkuyi, ya bayyana cewa zai ci gaba da baiwa dalibai tallafin gurbin karo karatu domin samun isasun likitoci a jihar  masamman likitoci mata.

Domin tunkarar hakan zai zama  kalubale ga rashin isasun likitoci mata da jihar  take fama dashi.\”zakaga cewa mace bata da lafiya a maimakon mace likita ta duba mara lafiyar sai kaga likita namiji ne zai tsaya a kan mara lafiyar sabo da rashin isassun  likitoci mata\’.
Sanata ya kuma kai wadannan dalibai mata su 10 gidan gwamnatin Jahar Kaduna domin gwamna ya gansu ya kuma sa masu albarka.

A nasa jawabin malam  Nasiru Elrufai, ya ce shima zai yi koyi da sanata hunkuyi zai bawa dalibai 30 gurbin karo karatu a kasashan waje.
Akarshe ya yi kira ga daliban da su mayar da hankali a kan  abin da ya kaisu kasar Uganda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here