An sace man fetur na biliyan 50 – NNPC

    0
    1275

    Usman Nasidi Daga Kaduna

    Kamfanin man fetur na Najeriya NNPC, ya ce an yi asarar lita miliyan
    531 na man fetur wanda kudinsa ya kama naira biliyan 50, sakamakon
    barnar da barayin bututun mai suka yi tsakanin watannin Janairu da
    Satumbar 2015, a wasu layukan bututu da aka shimfida su daga jihar
    Legas zuwa birnin Ilorin.

    A wani jawabi da ta gabatar a gaban kwamitin man fetur na majalisar
    dattawan kasar, Manajan Daraktar hukumar kula da bututun mai na
    kamfanin PPMC, uwargida Esther Nnamdi Ogbue, ta ce asarar da aka samu
    ta faru ne sakamakon fashe-fashen bututun man fetur a yankunan Arepo
    da Mosimi, wanda hakan ya sanya ake samun matsalar fitar da man.

    Uwargida Nnamdi-Ogbue ta ce duk da
    kalubalen da ake fuskanta a layukan bututun da aka shimfida daga Lagss
    zuwa birnin Ilorin din, PPMC zai ci gaba da kokarin tabbatar da cewa
    kasar ta samu isasshen man fetur din da ake bukata wajen loda mai daga
    daffo din dake Lagos da Oghara da kuma na baya-bayan nan da ke
    Calabar.

    Kazalika, Shugabar hukumar PPMC ta kara da cewa wasu dillalan mai
    marasa kishin kasa ne ke dakile kokarin da hukumar ke yi na kawar da
    layuka a gidajen mai a fadin kasar, inda suke ayyukan da basu dace ba,
    kamar sayar da man a kasuwannin bayan fage.

    Hukumar ta tabbatar da cewa tana duba hanyoyin da za ta bi wajen
    tabbatar da cewa an samu mafita ta din-din-din ga wannan matsala ta
    rashin mai, inda ta ce akwai bukatar a gina wani rumbu na adana
    isasshen man fetur.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here