Usman Nasidi Daga Kaduna
Kamfanin man fetur na Najeriya NNPC, ya ce an yi asarar lita miliyan
531 na man fetur wanda kudinsa ya kama naira biliyan 50, sakamakon
barnar da barayin bututun mai suka yi tsakanin watannin Janairu da
Satumbar 2015, a wasu layukan bututu da aka shimfida su daga jihar
Legas zuwa birnin Ilorin.
A wani jawabi da ta gabatar a gaban kwamitin man fetur na majalisar
dattawan kasar, Manajan Daraktar hukumar kula da bututun mai na
kamfanin PPMC, uwargida Esther Nnamdi Ogbue, ta ce asarar da aka samu
ta faru ne sakamakon fashe-fashen bututun man fetur a yankunan Arepo
da Mosimi, wanda hakan ya sanya ake samun matsalar fitar da man.
Uwargida Nnamdi-Ogbue ta ce duk da
kalubalen da ake fuskanta a layukan bututun da aka shimfida daga Lagss
zuwa birnin Ilorin din, PPMC zai ci gaba da kokarin tabbatar da cewa
kasar ta samu isasshen man fetur din da ake bukata wajen loda mai daga
daffo din dake Lagos da Oghara da kuma na baya-bayan nan da ke
Calabar.
Kazalika, Shugabar hukumar PPMC ta kara da cewa wasu dillalan mai
marasa kishin kasa ne ke dakile kokarin da hukumar ke yi na kawar da
layuka a gidajen mai a fadin kasar, inda suke ayyukan da basu dace ba,
kamar sayar da man a kasuwannin bayan fage.
Hukumar ta tabbatar da cewa tana duba hanyoyin da za ta bi wajen
tabbatar da cewa an samu mafita ta din-din-din ga wannan matsala ta
rashin mai, inda ta ce akwai bukatar a gina wani rumbu na adana
isasshen man fetur.