Gwamnatin za ta farfado da sufurin jiragen sama a Nijeriya

    0
    1854

    Isah Ahmed Daga Jos

    Ministan kasa a ma\’aikatar harkokin sufurin jiragen sama ta tarayya,
    Sanata Hadi Sirika ya bayyana cewa gwamnatin tarayya zata farfado da
    harkokin  sufurin jiragen sama a Nijeriya.

    Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron harkokin sufurin jiragen sama
    na  duniya, da aka  gudanar a birnin Montreal, na kasar Kanada.
    Ya ce wannan gwamnati ta Nijeriya,  karkashin shugaban kasa Muhammad
    Buhari ta kuduri aniyar sake farfaxo da harkokin sufurin jiragen sama
    a Nijeriya, ta hanyar gyara tashoshin jiragen saman kasar da tare da
    samar kayayyakin aiki irin na zamani  a tashoshin.

    Ya ce gwamnatin Nijeriya zata yi hakan ne don ganin ta tafi tare da manyan kasashen
    duniya, da suka cigaba kan harkokin sufurin jiragen sama.

    A nasu jawaban daban daban a wajen taron  ministan sufuri na kasar
    Kanada Marc Garneau da ministan sufuri na kasar Kolombiya da sakatare
    janar na kungiyar yawon bude ido  ta duniya [UNWTO] sun bukaci
    kasashen duniya su hada kai, don ganin an aiwatar da tsare tsare
    bunkasa harkokin sufurin jiragen sama a duniya, don amfanin al\’ummar
    duniya.

    Shi dai wannan taro ministan kasa a ma\’aikatar sufurin jiragen sama ta
    tarayya Sanata Hadi Sirika ne ya jagoranci tawagar Nijeriya, wadda ta
    kun shi jakadan Nijeriya na riko a kasar Kanada  Jafar Mohammed  da
    daraktocin ma\’aikatar harkokin sufurin jiragen sama ta Nijeriya kuma taron  ya sami halartar wakilai daga  kasashen duniya 99.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here