PDP Ta Bukaci A Saki Olise metuh

    0
    1452

    Rabo Haladu Daga Kaduna
    Cikin sanarwan dake dauke da sa hannun sakataren
    jamiyyar PDP na Kasa Farfesa Adewole
    Oladipo PDP ta bukuci
    hukumar EFCC ta gaggauta sako mata
    kakakin ta Mr Oliseh Metuh da ake zargi
    da halarta kudin haram sama da naira
    miliya dubu.
    Jamiyyar ta PDP
    tace kame Oliseh Metuh bai zo mata da
    mamaki ba idan akayi la’akari da
    barazanar da aka ce yasha huskanta daga
    jamniyyar APC dama gwamnatin tarayya
    wadda tace ta shiga rudani kuma take
    kokarin rufe bakin ‘yan adawa sai dai mataimakin kakakin jam’iyyar
    Barister Abdullahi Jalo
    a cewar sa
    ‘’PDP tasha fadin cewa tana goyon bayan
    hana cin hanci a Najeriya, shin a Oliseh
    Metuh gayyatar sa da aka yi abinda
    yakamata kowa ya sani cewan idan an
    kama mutum cewa akayi akai shi kotu
    kada ya wuce awa 24.Ai babu wanda zaice
    maka an same shi da laifi kotu ce take da
    wannan hurumin mu jira muji kotu me
    zata yi, EFCC ai ba kotu bace haka kuma
    maganganun cikin gari ba kotu bane’’
    Sai dai da aka tambayi Barister cewa
    sakataren jamiyyar tasu yace kame Oliseh
    Metu bita da kulli ne?.
    Anan ko sai yace bai yiyuwa Sakatare na
    magana shi ma yana Magana.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here