A Ci Gaba Da Kama Yayan PDP-Jalo

    0
    1259

    Rabo Haladu Daga Kaduna Jam\’iyyar PDP ta bukaci hukumar
    EFCC ta ci gaba da kama mambobinta da
    ake zargi da hannu wajen karbar kudin
    sayen makamai. Mataimakin Sakataran jamiyyar PDP Barrister Abdullahi Jallo ne yabayyanawa taron manema labari haka a Abuja.
    Sai dai yace zargin da ake yi wa wasu \’ya\’yan
    jam\’iyyar dangane da sama da fadi da kudin ba
    zai shafi martabar jam\’iyyar ba.
    Mataimakin Sakataren yada labaran Jam\’iyyar,
    Barrister Abdullahi Jallo ya ce, \”Wajibi ne
    mutane su sani cewa gwamnatin PDP da take
    mulki a wancan lokacin ta bayar da kudin
    sayen makamai. Ya kamata shugaban kasa ya
    tabbatar sun amayar da kudin\”.
    Barrister Jallo ya kuma bukaci hukumar EFCC
    ta daure duk dan jam\’iyyar PDP da kotu ta
    tabbatar ya ci moriyar kudin sayen makaman.
    Ya kara da cewa kashi tamanin bisa dari na
    \’yan jam\’iyyar PDP mutanen kirki ne, yana mai
    cewa bai kamata a dinga yi wa \’ya\’yan
    jam\’iyyar kudin-goro a kan zargin sama-da-fadi
    da kudaden kasa ba.
    A halin da ake ciki dai hukumar yaki da cin
    hanci da rashawa wato EFCC na tuhumar wasu
    ya \’yan jam\’iyyar da suka hada da tsohon
    shugaban PDP na kasa, Ahaji Bello Haliru da
    Kakakin jam\’iyyar Olisa Metuh da tsohon
    gwamnan jihar Sokoto, Attahiru Dalhatu
    Bafarawa kan wannan badakalar.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here