EFCC Ta Bayar Da Jafaru Isa A Hannun Beli

    0
    1127

    Rabo Haladu Daga Kaduna
    Tsohon gwamnan mulkin soja na jihar Kaduna,
    Lawal Jafaru Isa ya mayar da Naira Miliyan
    100 ga EFCC, da ake zargin tsohon mai bai
    wa shugaban Najeriya shawara kan
    harkokin tsaro Kanar Sambo Dasuki ya ba
    shi.
    Wani makusancin Jafaru Isa ya tabbatarwa da manema labarai haka a Abuja
    cewa an mika kudin ne ga hukumar EFCC.
    A makon jiya ne hukumar da ke yaki da masu
    yi wa tattalin arzikin kasa zagon-kasa, EFCC, ta
    kama Lawal Jafaru Isa.
    Ana tuhumarsa da karbar wani kaso daga cikin
    dala biliyan biyu na sayen makamai, zamanin
    mulkin tsohon shugaban Najeriya Goodluck
    Jonathan.
    Jafaru Isa shi ne mutum na farko a makusantan
    Shugaba Muhammadu Buhari da hukumar EFCC
    ta kama kan zargin badakalar cin hanci da
    rashawa.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here