karin farashin kananzir jam\’a na ci gaba da kokawa

    0
    1269

    Rabo Haladu Daga Kaduna \’Yan Nigeria suna ci gaba da mayar da
    martani kan karin farashin kananzir da
    gwamnati ta yi.
    A wannan makon ne dai gwamnati
    ta sanar da karin Naira 33 a kan kowace lita,
    ma\’ana ta tashi daga Naira 50 zuwa naira 83.
    Alhaji Bashir Dan Malam shi ne shugaban
    kungiyar masu gidajen Mai masu zaman kansu
    wato IPMAN a jihar Kano, ya shaidawa manema labarai
    cewa karin farashin ba shi da wata illa
    matukar za a samar da shi a duk fadin kasar.
    To sai dai Alhaji Lawal Muhammad Dan Zaki na
    kungiyar ta IPMAN na ganin karin bashi da
    wata fa\’ida, idan aka yi la\’akkari da karin da
    aka dade ana yi a kan man Fetur da shi
    Kananzir, amma har yanzu bai wadata a kasar
    ba.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here