Sarki Tafida Ya Bar Jam\’iyyar PDP

    0
    1531

    Rabo Haladu Daga Kaduna

    TSOHON jakadan Nijeriya a Birtaniya, Sanata Dalhatu Sarki Tafida, ya ce ya yanke shawarar barin jam\’iyyar PDP ne saboda a cewarsa ta rasa alkibla.
    Sanata sarki Tafida  ya kara da cewa a yanzu babu wani aiki da PDP take yi, a da can dai sun yi abin a zo a gani amma yanzu sai kwaso mutanen da bai dace ba
    jam\’iyyar ke yi.
    Ya kuma ce jam\’iyyar PDP ba ta bai wa mutane irinsa girma, ba kuma a daukar shawarar su sai dai abin da \’ya\’yan jam\’iyyar suka ga damar yi. Sanata Tafida ya ce kawo yanzu bai shiga kowace jam\’iyya ba, yana dai yin nazari don sanin inda ya dace ya nufa.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here