An Sake Haramta Shigowa Da Shinkafa Najeriya

    0
    1163

    sake haramta shigo da shinkafa
    Nigeria
    Rabo Haladu Daga Kaduna

    Hukumar hana fasa-kwauri ta Najeriya ta
    sake haramta shiga da shinkifa ta
    iyakokin da ba na ruwa ba.
    A watan Oktoban bara ne dai hukumar ta ba da
    damar shiga da shinkafar muddin za a biya
    kudin fito kamar yadda ya dace.
    Sai dai, a cewar hukumar, da farko kwalliya
    tana biyan kudin sabulu amma daga watan
    Janairun bana zuwa yanzu kudin shigar da ta
    samu naira biliyan daya da miliyan dari shida
    da tamanin bai kai abin da ya kamata a ce ta
    samu ba, don haka take zargin ana fasa
    kwaurin shinkafar.
    Kakakin hukumar hana fasa-kwauri ta Najeriya
    Wale Adeniyi ya shaidawa manema labarai ce wa a watan
    Oktobar shekarar da ta gabata ne aka amince a
    shigo da shinkafa ta iyakokin kasar, amma a
    yanzu an soke wannan shawara.
    Hakan na nufin an haramta shigo da ita ta
    iyakokin kasa da kuma ta tashoshin jiragen
    ruwa, an dauki matakin ne saboda an samu
    rahoton an shigo da shinkafa ta tasahr jirgin
    ruwa da ke Kwatano amma kuma ba a samu
    kudaden shigar da su suka kai yawan abin da aka shigo da su ba.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here