JABIRU A HASSAN, Daga kano.
Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta kano pillars sun nuna gamsuwarsu bisa yadda kungiyar take samun gagarumar nasara a wasannin da take bugawa na kakar wasanni ta bana.
Shugaban kungiyar magoya bayan kano pillars Alhaji Bashir Mu\’azu Jide shine ya sanar da haka bayan kungiyar ta kano pillars ta sami nasara kan takwararta ta Nasarawa united a fafatawar da suka yi ranar lahadin data gabata, inda ya jaddada cewa da yardar Allah, kano pillars zata sami nasarar lashe kofin firimiya na bana a karshen gasar.
Bashir Jide ya kuma yabawa kokarin bangaren masu horarwa bisa jagorancin Muhammadu Babaganaru da kuma shugaban kungiyar, Alhaji Kabiru Baita da kuma su kansu \’yan wasan saboda yadda aka hada hannu ana aiki tare.
Bugu da kari, ya godewa gwamnatin jihar kano saboda cikakken goyon bayan da take baiwa kungiyar ta kano pillars, wanda a cewar sa, hakan tana kwarara gwuiwar \’yan wasan da masu horar dasu da kuma magoya baya a kowane lokaci, tareda yin alkawarin cewa zai ci gaba