Yan Kasuwa Sun Kai Kashi 70 Na Ginin Rumfunansu A Kano

    0
    1145

    Jabiru A Hassan, Daga kano.

    Sakamakon  Iftila\’in  gobarar da ta faru a kasuwar sabon Garin Kano kwanakin baya, yanzu haka dai  \’yan kasuwar sun cimma kashi 70 daga cikin dari na aikin  sake ginin rumfunan su da suka kone.

    Wakilin mu  wanda ya ziyarci kasuwar, ya ruwaito cewa  \’yan kasuwar suna kokari matuka wajen gyaran rumfunan su , sannan  wasu ma har sun kammala aikin gyaran rumfunan nasu harma sun fara sanya kaya domin ci gaba da kasuwancin su kamar yadda aka saba.

    Tuni dai kungiyar \’yan kasuwar ta Sabon Garin Kano ta bayyana  godiyar ta ga gwamnatin jihar  kano saboda baiwa  \’yan kasuwar dama da tayi na su sake ginin rumfunan su da kansu  kamar yadda suka nema tun da farko.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here