Rundunar \’Yan Sanda Ta Karyata Rahoton An Mutu A Zaben Cike Gurbi

    0
    1098

    Jabiru A Hassan, Daga kano.

    RUNDUNAR \’yan  sanda ta Jihar Kano ta sanar da cewa ba a yi asarar rai ba a rikicin da ya faru  ranar zaben cike gurbi na karamar hukumar Minjibir.
    A cikin sanarwar, wadda kakakin rundunar, Malam Magaji Musa Majiya  ya sanya wa hannu kuma aka raba wa manema labarai, ya nunar da cewa babu kisan kai a rikicin sannan wadanda ma suka sami raunuka tuni aka sallame su daga asibitocin da suke bayan sun murmure.
    Bisa haka ne  rundunar ta bukaci kafafen yada labarai da su rika  tantance rahotanni  da labarai kafin su fitar da su domin tabbatar da sahihancin su  a kodayaushe.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here