Bayan Sanya Wa Kasafin Kudi Hannu Sai______

    0
    1218

     

    Jabiru A Hassan, Daga Kano.

    SANYA hannu kan kasafin kudin shekara ta  2016 zai  bai wa gwamnatin tarayya damar aiwatar da manufofin ta  na ci gaban kasa ta yadda al\’umma za su sami saukin kuncin rayuwa da ake ciki.
    Wannan tsokaci ya fito ne daga Alhaji Usman Dan Gwari, wani jigo a harkar hada-hadar kayan gwari da dillancin su, sannan ya nunar da cewa wannan kasafin kudi zai  kasance irin sa na farko a kasar nan idan aka dubi irin gwagwarmayar da aka yi kafin ya sami amincewr shugaban kasa.
    Haka kuma ya yi fatar cewa za a bude sabon shafi na dangantaka mai kyau tsakanin bangaren zartaswa  da kuma majalisa musamman ganin cewa idan akwai fahimtar juna tsakanin wadannan bangarori guda biyu  za a sami damar gudanar da ayyuka na alheri ga al\’umma kamar yadda ake ta tsammani.
    Daga karshe, Ahaji Usman Dan Gwari ya yi fatar cewa \’yan Nijeriya za su sami ingancin rayuwa idan har suka kara yin hakuri , sannan ya yi fatar Allah ya kara hada kan majalisa da bangaren zartaswa ta yadda aiki zai tafi kamar yadda ake bukata.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here