Isah Ahmed Daga Jos
Alhaji Sale Bayari shi ne sakataren sabuwar kungiyar nan ta ci gaban
al\’ummar fulani a Nijeriya [GAFDAN] kuma tsohon sakataren kungiyar
fulani makiyaya ta miyetti Allah ta Nijeriya.
A wannan tattaunawa da ya yi da wakilinmu kan zarge-zargen da ake yi wa
al\’ummar fulani kan tashe-tashen hankula a Nijeriya, ya kare al\’ummar
fulanin kan wadannan zarge-zarge da ake yi masu, tare da kawo
shawarwari kan hanyoyin da za a warware wadannan matsaloli.
Ga yadda tattaunawar ta kasance:
GTK; Mane ne za ka ce kan zarge-zargen da ake yi wa al\’ummar fulani kan
kai hare-hare a Nijeriya?
Sale Bayari; To, abubuwan da kowa ya sani ne a Nijeriya, cewa a cikin
shekaru 16 da suka gabata na mulkin farar hula. An koma wata irin
rayuwa ta siyasa wadda wasu suka dauka idan ba su hargitsa al\’amura a
addinance ko a kabilance ba, ba za su ci zabe ba. Wannan shi ne ya
jawo mana rikice-rikice iri-iri a Nijeriya, musamman a yankin arewa
ta tsakiya da wasu suke kira Midle Belt.
A wannan yanki na arewa ta tsakiya aka dauko wani ra\’ayi na kiyayya ga
al\’ummar hausawa da fulani aka sanya su a gaba. Ko ana jihar Filato
a lokacin da aka yi rikicin Jos na ranar 7 ga watan 9 na shekara ta
2001, ta\’adin da aka yiwa al\’ummarmu a irin yankunan Barikin Ladi
da Riyom da Jos ta Kudu suna da yawa.
A lokacin da aka kira mu gaban kwamitin binciken wannan rikici na Mai
shari\’a Niki Tobi mun kai lissafin mutanen da aka kashe mana a wannan
rikici na mata da qananan yara. A lokacin ne aka gano cewa a kashi 70
bisa 100 na mutanen da aka kashe a wannan rikici mutanenmu ne.
Ko a farar takardar da tsohon gwamnan jihar Filato Jonah Jang ya fitar
kan wannan rikici, a shekara ta 2009 ya nuna irin dibbin mutanen da
aka kashe mana a wadannan yankuna.
A lokacin \’yan kudu saboda suna da jaridu sai aka sami hadin kai na
bangaren qabilanci da bangaren addini, kafin kace haka sai masu neman
kuri\’a a arewa suka zo suka hade da wasu mutanen arewa. Sai ya
zamanto a lokacin tun da shugabannin kasar daga kudu suke, sai suka
rika amfani da irin wadannan rikice-rikice. Kowa ya zamanto yana
amfani da siyasar kabilanci da addini a lokacin don samun biyan
bukata.
Duk inda ake zargin fulani da rikice-rikice idan ka duba zaka ga akwai
kabilanci da addini a ciki. Kuma duk abin da ya faru idan kai ba
Bafulatani ne ko kuma kai Bahaushe ne ba za a ji komai ba. Amma idan
kai wani yare ne dan arewa ko dan kudu idan wani abu ya same ka, sai
ka ji Nijeriya baki daya ta amsa.
A shekara ta 2013 an kira mu a majalisar wakilai ta tarayyar Nijeriya,
a inda ake son a yi dokar samun burtali da makiyaya ga fulani makiyaya
a Nijeriya. Muka je muka gabatar da dalilan da suka sanya muke sun a
samar da burtaloli da wuraren kiwo ga fulani makiyaya a Nijeriya.
Kafin ka ce kwabo sai aka mayar da wannan abu zuwa ga addini haka \’yan
arewa wadanda ba musulmi ba, da \’yan kudu wadanda ba musulmi ba, suka
hade aka dakile wannan doka.
Idan ana son a zauna lafiya kuma dukkanmu mun yarda cewa mu \’yan
Nijeriya ne, abin da ya sami wani daga cikinmu ko na alheri ko na
bakin ciki ya shafi kowa daga cikinmu.
Duk inda ka ji an taba Bafulatani idan ba a mayar da hankali ba. Ko
bajima ko badade za ka ji wani abu ya faru a wajen. Saboda haka nake
gaya wa jama\’a cewa idan kun ji Bafulatani ya taba wasu mutane a wani
waje to a tambaya mutanen nan su fadi gaskiya tsakaninsu da Allah ba su
yiwa fulanin nan wani abu ba?
Domin gaskiyar magana idan ka sami fulani sun je sun taba wasu mutane
a wani wuri to a binciki wadannan mutanen su fadi mene ne suka
yiwa fulanin? Idan suka ce basu yi masu komai ba, to wannan abin da
aka yi masu ba fulani ba ne, wasu ne daban.
GTK; Wato a ganinka irin takurawar da ake yi wa fulani a kasar nan ne
yake kawo wadannan rikice-rikice da suke faruwa?
Sale Bayari; Kwarai kuwa domin takurawar da ake yi wa fulani a Nijeriya
ta kai inda ta kai. Domin akwai takurawar da fulani suke fuskanta a
Nijeriya ta irin yanayin yau akwai kuma takurawa ta muhalli, da Allah
ya kawo. Wato kamar dumamar yanayi da Allah ya kawo domin a yau duk
inda ake zaune a duniya za ka ga mutanen da suke zama a arewa suna
kaura suna suna komawa kudu, saboda ruwa yana da ta barin arewa yana
komawa kudu.
Don haka a yau mutanen Nijar babu yadda za a yi su je arewa su ce za su
yi kiwo, sai dai su taho kudu don kiwo. Haka mutane Chadi da Mali da
Kamaru duk idan suka tashi kudu suke tahowa. Kuma babu yadda za a yi a
Nijeriya a ce wani dan Nijeriya ba zai je wani waje ya zauna ba. A da
fulanin da suke zaune a Sakkwato da Zamfara da Katsina da Jigawa da
dai sauransu ruwan da ke wuraren ya ishe su rani da damina. Amma yanzu
baki daya wadannan wurare sun bushe saboda canjin yanayi na muhalli.
Saboda haka manoma yanzu ba sa samun amfanin gona kamar yadda suke samu
a da.
Saboda haka babu yadda za a yi makiyayi ya zauna wurin da babu ruwa da
ciyawa. Kuma a ce bafulatani bai isa ya je kudu ba. duk da cewa duk
Nijeriya ce. Alhalin suma mutanen kudu suna tashi suna zuwa ko\’ina a
Nijeriya suna gudanar da harkokinsu. Suna zuwa Maiduguri da Sakkwato
da Adamawa da Kano suna harkokinsu.
GTK; Mane ne za ka ce kan umarnin da shugaban kasa Muhammad Buhari ya
bai wa Babban Sifeto Janar na \’Yan sanda Nijeriya kan a kamo wadanda
suka kai hari kwanakin baya a yankin Iyamurai wadanda ake zargin
fulani ne?
Sale Bayari; Ni a wurina wannan umarni da shugaban kasa ya bayar ya yi
daidai. Duk inda dan ta\’adda da mai laifi yake idan aka ce a je a kamo
shi, wannan ba laifi ba ne. Tun da ba an ce a je a hallaka shi ba ne kamar
yadda ake yi mana.
Ana yi mana zargi cewa fulani suna fyade da sata da fashi da barna kan
wannan sai a je a far masu a kashe su. To ko da fulani suna fyade da
fashi da sata kamar yadda kowace al\’umma take yi. Fashi da sata da
fyade da satar mutane a wajen mutanen kudu aka fara gani a Nijeriya.
Yanzu a kudu akwai inda ake barbarar \’yaya mata suna haihuwar jarirai
ana sayarwa kamar yadda ake kiwon kaji.
Don haka idan shugaban kasa ya ce duk wanda ya yi laifi a kasar nan a
kama shi, ya yi daidai saboda za yi bincike ne kafin a kai kotu.
Sai dai kawai abin da zan fada a nan shi ne a matsayinsa na shugaban
kasa yana da kyau dama wannan aiki ne na jami\’an tsaro ba sai shugaban
kasa ya fito ya bada umarnin a je a kama masu laifi ba. Idan aka ce
sai shugaban kasa ya ce a je a kama masu laifi a cikin kashi 100 ba za
a kama kashi 10 ba.
Domin shugabannin kasar nan da suka gabata ba su yi haka ba, tun daga
lokacin tsohon shugaban kasa Obasanjo har ya zuwa ga tsohon shugaban
kasa Jonathan ana rikici tsakanin fulani da manoma, amma babu wani da
ya ce a je a kama manoma ko makiyaya. Mu mun sani an zo ne an uzura
wa shugaban kasa Buhari, domin ana son a nata shi, saboda ana ganin
shi Bafulatani ne saboda haka ya kamata ya dauki wannan mataki a kan
abin da fulani suke yi. Mu kuma muna ganin abin ba haka yake ba, domin
duk wani da ya yi laifi a kasar nan shugaban kasa ya wuce ya ce shi ga
kabilarsa ko ga addininsa, shi shugaban kasa na kowa ne. Kuma
hakkinsa ne ya kare kowa a Nijeriya saboda haka muna kira duk inda aka
taba fulani shugaban kasa ya bada umarnin a je a bincika a kamo wadanda
suka taba fulanin. Kuma duk inda ake zargin cewa bafulatani ya je ya
yi wani abu ya bada umarni kamar yadda ya bada wannan umarnin a je a
nemo bafulatanin da ya yi wannan laifi a bincika a yi masa hukumci.
GTK; A kwanakin baya gwamnonin arewa sun fara tattaunawa kan shirin
killace fulani a wuri daya, don magance wadannan matsaloli. Mane ne
ra\’ayinka kan wannan al\’amari?
Sale Bayari; A kullum nakan ce masu wannan magana ta killace fulani
ba su fahimci mane ne ake nufi da killace fulani ba. Domin na san maganar
a killace fulani a kasar Amurka aka fara ta, tun a shekara ta 1880,
amma har yanzu akwai fulani makiyaya da suke yawo a kasar ta Amurka.
Kuma a duk duniya musamman a nan Afrika babu inda aka killace fulani
aka ce dole su zauna a wuri daya. Akwai makiyaya a Afrika ta Kudu
akwai makiyaya a Afrika ta Tsakiya akwai makiyaya a Afrika ta Yamma,
amma babu inda aka taba killace fulani a wuri daya aka ce dole su
zauna a wuri Daya. Saboda haka wannan abu ba zai yiwu ba a Nijeriya.
GTK; Wadanne hanyoyi ne kake ganin za a bi a warware wadannan matsaloli?
Sale Bayari; To kamar yadda na gaya maka ne mun yi kamar shekaru 7
muna kokarin ganin an samarwa da fulani makiyaya a Nijeriya,
burtaloli da wuraren kiwo. Misali a duk lokacin makiyayi zai tashi
daga makiyaya ta yankin Wase zai zo makiyaya ta yankin Mangu a jihar
Filato. Za a iya sanin ya taso ne daga makiyaya ta yankin Wase saboda
tana karkashin hukuma. Lokacin da ya taso daga yankin Wase za a iya
gayawa masu kula da makiyaya ta yankin Mangu. In zama zai yi an san da
shigowarsa da zaman da zai yi, idan zai wuce ne an san inda zai wuce.
Ka ga kowanne Bafulatanin da yake kiwo an san da zamansa. Wannan shi ne
zai magance wadannan matsaloli.
GTK; Karshe wanne sako ne kake da shi zuwa ga gwamnati dangane da
wadannan al\’amura na fulani?
Sale Bayari; Sako na ga gwamnati shi ne ta gaya wa majalisar tarayya
cewa suna da hakki su tabbatar da kowanne dan Nijeriya yana da kariya.
Wadannan fulani da ake magana ba su wasu da wata sana\’a da ta wuce
kiwon dabbobinsu. Saboda haka a shirye suke su bayar da rayukansu kan
wadannan dabbobi nasu. Don haka dole ne a dubi hakkin fulani a kasar
nan, a daina kyamarsu a ba su ‘yancinsu domin suma \’yan Nijeriya.
Isah Ahmed Daga Jos
Alhaji Sale Bayari shi ne sakataren sabuwar kungiyar nan ta ci gaban
al\’ummar fulani a Nijeriya [GAFDAN] kuma tsohon sakataren kungiyar
fulani makiyaya ta miyetti Allah ta Nijeriya.
A wannan tattaunawa da ya yi da wakilinmu kan zarge-zargen da ake yi wa
al\’ummar fulani kan tashe-tashen hankula a Nijeriya, ya kare al\’ummar
fulanin kan wadannan zarge-zarge da ake yi masu, tare da kawo
shawarwari kan hanyoyin da za a warware wadannan matsaloli.
Ga yadda tattaunawar ta kasance:
GTK; Mane ne za ka ce kan zarge-zargen da ake yi wa al\’ummar fulani kan
kai hare-hare a Nijeriya?
Sale Bayari; To, abubuwan da kowa ya sani ne a Nijeriya, cewa a cikin
shekaru 16 da suka gabata na mulkin farar hula. An koma wata irin
rayuwa ta siyasa wadda wasu suka dauka idan ba su hargitsa al\’amura a
addinance ko a kabilance ba, ba za su ci zabe ba. Wannan shi ne ya
jawo mana rikice-rikice iri-iri a Nijeriya, musamman a yankin arewa
ta tsakiya da wasu suke kira Midle Belt.
A wannan yanki na arewa ta tsakiya aka dauko wani ra\’ayi na kiyayya ga
al\’ummar hausawa da fulani aka sanya su a gaba. Ko ana jihar Filato
a lokacin da aka yi rikicin Jos na ranar 7 ga watan 9 na shekara ta
2001, ta\’adin da aka yiwa al\’ummarmu a irin yankunan Barikin Ladi
da Riyom da Jos ta Kudu suna da yawa.
A lokacin da aka kira mu gaban kwamitin binciken wannan rikici na Mai
shari\’a Niki Tobi mun kai lissafin mutanen da aka kashe mana a wannan
rikici na mata da qananan yara. A lokacin ne aka gano cewa a kashi 70
bisa 100 na mutanen da aka kashe a wannan rikici mutanenmu ne.
Ko a farar takardar da tsohon gwamnan jihar Filato Jonah Jang ya fitar
kan wannan rikici, a shekara ta 2009 ya nuna irin dibbin mutanen da
aka kashe mana a wadannan yankuna.
A lokacin \’yan kudu saboda suna da jaridu sai aka sami hadin kai na
bangaren qabilanci da bangaren addini, kafin kace haka sai masu neman
kuri\’a a arewa suka zo suka hade da wasu mutanen arewa. Sai ya
zamanto a lokacin tun da shugabannin kasar daga kudu suke, sai suka
rika amfani da irin wadannan rikice-rikice. Kowa ya zamanto yana
amfani da siyasar kabilanci da addini a lokacin don samun biyan
bukata.
Duk inda ake zargin fulani da rikice-rikice idan ka duba zaka ga akwai
kabilanci da addini a ciki. Kuma duk abin da ya faru idan kai ba
Bafulatani ne ko kuma kai Bahaushe ne ba za a ji komai ba. Amma idan
kai wani yare ne dan arewa ko dan kudu idan wani abu ya same ka, sai
ka ji Nijeriya baki daya ta amsa.
A shekara ta 2013 an kira mu a majalisar wakilai ta tarayyar Nijeriya,
a inda ake son a yi dokar samun burtali da makiyaya ga fulani makiyaya
a Nijeriya. Muka je muka gabatar da dalilan da suka sanya muke sun a
samar da burtaloli da wuraren kiwo ga fulani makiyaya a Nijeriya.
Kafin ka ce kwabo sai aka mayar da wannan abu zuwa ga addini haka \’yan
arewa wadanda ba musulmi ba, da \’yan kudu wadanda ba musulmi ba, suka
hade aka dakile wannan doka.
Idan ana son a zauna lafiya kuma dukkanmu mun yarda cewa mu \’yan
Nijeriya ne, abin da ya sami wani daga cikinmu ko na alheri ko na
bakin ciki ya shafi kowa daga cikinmu.
Duk inda ka ji an taba Bafulatani idan ba a mayar da hankali ba. Ko
bajima ko badade za ka ji wani abu ya faru a wajen. Saboda haka nake
gaya wa jama\’a cewa idan kun ji Bafulatani ya taba wasu mutane a wani
waje to a tambaya mutanen nan su fadi gaskiya tsakaninsu da Allah ba su
yiwa fulanin nan wani abu ba?
Domin gaskiyar magana idan ka sami fulani sun je sun taba wasu mutane
a wani wuri to a binciki wadannan mutanen su fadi mene ne suka
yiwa fulanin? Idan suka ce basu yi masu komai ba, to wannan abin da
aka yi masu ba fulani ba ne, wasu ne daban.
GTK; Wato a ganinka irin takurawar da ake yi wa fulani a kasar nan ne
yake kawo wadannan rikice-rikice da suke faruwa?
Sale Bayari; Kwarai kuwa domin takurawar da ake yi wa fulani a Nijeriya
ta kai inda ta kai. Domin akwai takurawar da fulani suke fuskanta a
Nijeriya ta irin yanayin yau akwai kuma takurawa ta muhalli, da Allah
ya kawo. Wato kamar dumamar yanayi da Allah ya kawo domin a yau duk
inda ake zaune a duniya za ka ga mutanen da suke zama a arewa suna
kaura suna suna komawa kudu, saboda ruwa yana da ta barin arewa yana
komawa kudu.
Don haka a yau mutanen Nijar babu yadda za a yi su je arewa su ce za su
yi kiwo, sai dai su taho kudu don kiwo. Haka mutane Chadi da Mali da
Kamaru duk idan suka tashi kudu suke tahowa. Kuma babu yadda za a yi a
Nijeriya a ce wani dan Nijeriya ba zai je wani waje ya zauna ba. A da
fulanin da suke zaune a Sakkwato da Zamfara da Katsina da Jigawa da
dai sauransu ruwan da ke wuraren ya ishe su rani da damina. Amma yanzu
baki daya wadannan wurare sun bushe saboda canjin yanayi na muhalli.
Saboda haka manoma yanzu ba sa samun amfanin gona kamar yadda suke samu
a da.
Saboda haka babu yadda za a yi makiyayi ya zauna wurin da babu ruwa da
ciyawa. Kuma a ce bafulatani bai isa ya je kudu ba. duk da cewa duk
Nijeriya ce. Alhalin suma mutanen kudu suna tashi suna zuwa ko\’ina a
Nijeriya suna gudanar da harkokinsu. Suna zuwa Maiduguri da Sakkwato
da Adamawa da Kano suna harkokinsu.
GTK; Mane ne za ka ce kan umarnin da shugaban kasa Muhammad Buhari ya
bai wa Babban Sifeto Janar na \’Yan sanda Nijeriya kan a kamo wadanda
suka kai hari kwanakin baya a yankin Iyamurai wadanda ake zargin
fulani ne?
Sale Bayari; Ni a wurina wannan umarni da shugaban kasa ya bayar ya yi
daidai. Duk inda dan ta\’adda da mai laifi yake idan aka ce a je a kamo
shi, wannan ba laifi ba ne. Tun da ba an ce a je a hallaka shi ba ne kamar
yadda ake yi mana.
Ana yi mana zargi cewa fulani suna fyade da sata da fashi da barna kan
wannan sai a je a far masu a kashe su. To ko da fulani suna fyade da
fashi da sata kamar yadda kowace al\’umma take yi. Fashi da sata da
fyade da satar mutane a wajen mutanen kudu aka fara gani a Nijeriya.
Yanzu a kudu akwai inda ake barbarar \’yaya mata suna haihuwar jarirai
ana sayarwa kamar yadda ake kiwon kaji.
Don haka idan shugaban kasa ya ce duk wanda ya yi laifi a kasar nan a
kama shi, ya yi daidai saboda za yi bincike ne kafin a kai kotu.
Sai dai kawai abin da zan fada a nan shi ne a matsayinsa na shugaban
kasa yana da kyau dama wannan aiki ne na jami\’an tsaro ba sai shugaban
kasa ya fito ya bada umarnin a je a kama masu laifi ba. Idan aka ce
sai shugaban kasa ya ce a je a kama masu laifi a cikin kashi 100 ba za
a kama kashi 10 ba.
Domin shugabannin kasar nan da suka gabata ba su yi haka ba, tun daga
lokacin tsohon shugaban kasa Obasanjo har ya zuwa ga tsohon shugaban
kasa Jonathan ana rikici tsakanin fulani da manoma, amma babu wani da
ya ce a je a kama manoma ko makiyaya. Mu mun sani an zo ne an uzura
wa shugaban kasa Buhari, domin ana son a nata shi, saboda ana ganin
shi Bafulatani ne saboda haka ya kamata ya dauki wannan mataki a kan
abin da fulani suke yi. Mu kuma muna ganin abin ba haka yake ba, domin
duk wani da ya yi laifi a kasar nan shugaban kasa ya wuce ya ce shi ga
kabilarsa ko ga addininsa, shi shugaban kasa na kowa ne. Kuma
hakkinsa ne ya kare kowa a Nijeriya saboda haka muna kira duk inda aka
taba fulani shugaban kasa ya bada umarnin a je a bincika a kamo wadanda
suka taba fulanin. Kuma duk inda ake zargin cewa bafulatani ya je ya
yi wani abu ya bada umarni kamar yadda ya bada wannan umarnin a je a
nemo bafulatanin da ya yi wannan laifi a bincika a yi masa hukumci.
GTK; A kwanakin baya gwamnonin arewa sun fara tattaunawa kan shirin
killace fulani a wuri daya, don magance wadannan matsaloli. Mane ne
ra\’ayinka kan wannan al\’amari?
Sale Bayari; A kullum nakan ce masu wannan magana ta killace fulani
ba su fahimci mane ne ake nufi da killace fulani ba. Domin na san maganar
a killace fulani a kasar Amurka aka fara ta, tun a shekara ta 1880,
amma har yanzu akwai fulani makiyaya da suke yawo a kasar ta Amurka.
Kuma a duk duniya musamman a nan Afrika babu inda aka killace fulani
aka ce dole su zauna a wuri daya. Akwai makiyaya a Afrika ta Kudu
akwai makiyaya a Afrika ta Tsakiya akwai makiyaya a Afrika ta Yamma,
amma babu inda aka taba killace fulani a wuri daya aka ce dole su
zauna a wuri Daya. Saboda haka wannan abu ba zai yiwu ba a Nijeriya.
GTK; Wadanne hanyoyi ne kake ganin za a bi a warware wadannan matsaloli?
Sale Bayari; To kamar yadda na gaya maka ne mun yi kamar shekaru 7
muna kokarin ganin an samarwa da fulani makiyaya a Nijeriya,
burtaloli da wuraren kiwo. Misali a duk lokacin makiyayi zai tashi
daga makiyaya ta yankin Wase zai zo makiyaya ta yankin Mangu a jihar
Filato. Za a iya sanin ya taso ne daga makiyaya ta yankin Wase saboda
tana karkashin hukuma. Lokacin da ya taso daga yankin Wase za a iya
gayawa masu kula da makiyaya ta yankin Mangu. In zama zai yi an san da
shigowarsa da zaman da zai yi, idan zai wuce ne an san inda zai wuce.
Ka ga kowanne Bafulatanin da yake kiwo an san da zamansa. Wannan shi ne
zai magance wadannan matsaloli.
GTK; Karshe wanne sako ne kake da shi zuwa ga gwamnati dangane da
wadannan al\’amura na fulani?
Sale Bayari; Sako na ga gwamnati shi ne ta gaya wa majalisar tarayya
cewa suna da hakki su tabbatar da kowanne dan Nijeriya yana da kariya.
Wadannan fulani da ake magana ba su wasu da wata sana\’a da ta wuce
kiwon dabbobinsu. Saboda haka a shirye suke su bayar da rayukansu kan
wadannan dabbobi nasu. Don haka dole ne a dubi hakkin fulani a kasar
nan, a daina kyamarsu a ba su ‘yancinsu domin suma \’yan Nijeriya.