Wasu Matasa Sun Kona Gidan Kabiru Gaya

0
1624

Jabiru A Hassan, Daga kano.

Wasu fusatattun matasa sun kone gidan sanatan kano ta kudu Alhaji Kabiru Gaya da na dan majalisar wakilai mai wakiltar Gaya Abdullahi Mahmoud saboda kin cika alkawuran da suka daukar masu lokacin yakin neman zabe.

Wakilinmu wanda ya ziyarci karamar hukumar ya ruwaito cewa  matasan  sun yi wani yunkuri  na kone gidan shugaban karamar hukumar ta Gaya, amma  jami\’an  tsaro suka dakile wannan yukuri, kuma  matasan sun sanar da cewa sun  dauki wannan  mataki ne saboda su nuna fushin su   kan halin ko in kula da wakilan guda biyu suke nunawa   a karamar hukumar, sannan sun bayyana matakin da cewa shine mafi dacewa.

Wani matashi Abdullahi Garba wanda  bai shiga zanga-zangar ba, ya shaidawa Gaskiya Tafi Kwabo cewa yanzu fa kan mutane ya waye, don haka yana da kyau masu rike da madafun iko su rika cika alkawuran da suke yiwa al\’umominsu ko kuma su rika haduwa da fushin matasa kan rashin cika alkawari.

Tuni dai  rundunar \’yan sanda ta jihar kano ta dauki matakai na tsaro a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here