Ya Nemi Gwamna Ganduje Da Ya Kammala Titin Nan Mai Tsawon Kilomita 5

0
1157

Ya Nemi Gwamna Ganduje Da Ya Kammala Titin Nan Mai Tsawon Kilomita 5

Jabiru A Hassan, Daga Kano.

AN roki Gwamnan Jihar Kano, Dokta Abdullahi Umar Ganduje da ya fara kammala ayyukan nan na tituna masu tsawon kilo mita 5 wanda tsohuwar gwamnatin Kwankwaso ta fara amma har ya zuwa wannan lokaci ba a kammala su ba.
Wani  matashi Malam Umar Maigata shi ne ya yi wannan rokon , sannan ya nunar da cewa  wannan aiki na kilomita 5 yana daukar hankalin al\’ummar Jihar Kano, don haka yana da kyau gwamnati mai ci ta yi kokarin kammala shi kamar yadda manufofin ta suke na kammala ayyukan da ta gada.
Malam Maigata ya bayyana cewa muddin ba a sami kammala wannan aiki ba, ko shakka babu za a gamu da ambaliyar ruwa a wasu kananan hukumomin Jihar Kano idan damina ta sauka, don haka ne ya yi kira ga gwamnati da ta hanzar ta bai wa lyan kwangilolin da suke wadannan ayyuku kudade  wadatattu  ta yadda za su ci gaba da aikin, inda kuma daga karshe ya jinjina wa Gwamna  Ganduje saboda kokarin da  gwamnatinsa  ke yi na bunkasa Jihar

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here