Rikicin Manoma Da Fulani Mutane 8 Sun Rasa Rayukansu

0
1190

USMAN NASIDI Data Kaduna

Akalla mutum takwas ne suka rasa rayukansu kuma da  dama suka ji raunuka sakamakon fada a tsakanin Fulani  makiyaya da manoma a garin Koh da ke karamar Hukumar  Girie a Jihar Adamawa.
Idan ba a manta ba a makon jiya a garin na Koh ’yan sanda  uku sun rasa rayukarsu a lokacin da suka je aikin tsaro don  kwantar da ke neman tashi a garin.
Karo na uku ke nan da fada yake barkewa a tsakanin  makiyaya da manoma a cikin wata shida da suka gabata.
Fadan farko ya faru ne a watan Janairu na bana, inda  mutum 40 suka rasa rayukansu har wani DPO wanda aka  kashe lokacin da yake aikin tsaro a garin binikland da ke  jihar.
Wadanda lamarin ya auku a kan idonsu sun ce fadan na  makon jiya, ya faru ne a lokacin da wadansu makiyaya suka  shiga gonar wani manomi dan garin Koh, inda manomin da
ke cikin gonar ya nemi taimako daga mutanen Koh.
Shaidun sun kara da cewa bayan ya nemi taimako sai  mutanen garin suka fito suka yi nasarar korar makiyayan,  lamarin da ya sa makiyayan suka dawo da tasu tawagar  domin yaqi da manoman Koh.
“Wadannan mutum takwas da suka rasu da kuma bakwai  da suka ji rauni an kai su asibitin Zinth da ke Yola domin su  samu kulawa amma akwai wadansu biyu da nake ganin da  qyar su sha,” inji daya daga cikin shaidun.
Wani dan siyasa da ke garin Koh, Mista P.P. Elisha ya  tabbatar da faruwar fadan, kuma ya ce ya rasa
’yan uwansa biyu a fadan wanda a cikinsu akwai dan sanda  daya.
Kakakin ’Yan sandan Jihar Adamwa, DSP Abubakar Othman  ya tabbatar da faruwar lamarin, sai dai ya ce mutum daya  ne kawai ya rasu a fadan na makiyaya da manoman.
Othman ya ce qura ta lafa domin an aike da ’yan sanda da  dama garin Koh saboda tabbatar da zaman lafiya. 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here