UWA DA \’YAR TA SUN DAMBACE A KAN SAURAYI

0
1836

DAGA USMAN NASIDI 

Wani abin kallo tamkar wasan kwaikwayo ya faru yayinda  wata mata bazawara mai yara 4 tayi dambe da yarinyarta  da ta Haifa a kan saurayi a Nyanya,Abuja.
Rahotanni sun nuna cewa matan guda 2, uwa da ‘ya sun  baiwa hammata iska saboda saurayi a gaban jama’a.

matan yar kudancin Najeriya ce ,ta na sayar da giya da  barasa ne a unguwar, kuma yarinyarta dalibar jami’ar Jihar  Nasarawa, duk da dai ba wanda ke da tabbacin yar  makaranta ce da gaske.
“Abin ban mamaki ne da aka mace yar kimanin shekaru 40  da kari ,ke dambe da hahuwar cikinta yar shekaru 22 a  gidan giya. Sunyi dambe ne sosai, har suka tara ma ansu  jama’a. sun keta kayan juna har ya kai kayan ciki ya rage a
jikinsu. Daga baya muka gano dalilin fadan, ashe wani  namiji ne ke soyayya da uwa da ‘ya yana faskanci da su.”

“Daga baya da aka samu sasanta su, aka tambayesu shin  menene dalilin damben, uwar ta yi skalauhiru har sai da yarinyar  ta ce mahaifiyarta ce ta kwace mata saurayinta da ke kula da  ita, yana daukan nauyin karatun ta.
Anata jawabin uwar yarinyar, cewa tayi abin da ya faru shi. e, ta shekara biyar rana soyayya da mutumin kafin ‘yarta ta Mata kwace.
Tace bai wuci shekara daya da mutumin ya fara kwanciya da ‘yar  ta ba.” 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here