Matasan Izala Na Karamar Hukumar Jos Sun Tallafa Wa Gidan Tarbiyyar Matasa Kangararru Da Kayayyakin Abinci

0
1201

Isah  Ahmed Daga Jos

KWAMITIN wa\’azin matasa na kungiyar Jama\’atu Izalatil Bid\’ah Wa\’iqamatis Sunnah ta kasa reshen karamar hukumar Jos ta Arewa, da ke
jihar Filato sun tallafawa yaran da suke gidan tarbiyar matasa Kangararru na Laranto Jos, mai suna Young Peoples Home da kayayyakinabinci.
Kayayyakin abincin da Kwamitin matasan ya kai tallafin sun hada da fulawa da garin simonbita da kuma akuya.
Da yake mika kayayyakin abincin  shugaban kwamitin matasan na karamar hukumar Jos ta Arewa  Ustaz  Muhammad Nasiru  Abubakar,  ya bayyana
cewa sun kawowa matasan wadannan kayayyakin abinci ne  su tallafa masu.
Ya yi kira ga matasan da ke wannan gida kan su sani cewa  an kawo su wannan gida  ne don su gyara halayensu.
\’\’Duk wanda aka ce ya gyara halinsa ya yi wani abu ne da bashi da kyau. Don haka kuyi kokari ku gyara halayenku. Ku gyara rayuwarku ku
zamanto mutane na gari don kuji dadin rayuwarku\’\’.
Shugaban matasan wanda  mataimakinsa Malam Mustafa Abubakar Usman [Dattijo] ya  wakilta ya yi  kira ga gwamnatin jihar Filato  ta  kara
gudunmawar da take bayarwa a wannan gida.
A nasa jawabin shugaban  gidan Mista Simon Walman ya bayyana cewa shi dai wannan gidan tarbiyar matasa Kangararru gwamnatin jihar Filato ce,
ta gina shi a shekara ta 1981 a nan garin Jos.
Ya ce  an gina  gida ne domin a tarbiyartar da yara matasa kangararru wadanda suka yi laifaffukan da za a gurfanar da su a gaban kotu. Amma
saboda  shekarunsu basu kai a yanke masu hukumci ba, ake kawo su gidan domin a basu tarbiya.
Ya ce a yanzu suna da yara 33 a wannan gida kuma  gwamnatin Filato ce ta ke daukar nauyin  gidan. Kuma akwai kungiyoyi da suke zuwa suna
taimakawa wannan gida.
Shugaban gidan wanda mataimakiyarsa Misis Comfort Ibrahim  ta wakilta ya mika godiyarsu ga wannan qungiya kan wannan ziyara da taimakon  da
suka kawo masu.
\’\’A gaskiya mun yi godiya kan wannan taimakon abinci da kuka kawo mana.  Kuma mun yi godiya kan irin jawaban tarbiyar da kuka yi mana.
Babu shakka wadannan jawabai zasu taimakawa wadannan yara damu gabaki daya\’\’.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here