Za A Kafa Hukumar Arewa Maso-Gabashin Najeriya

    0
    960

    Rabo Haladu Daga  Kaduna

    MAJALISAR dattawan Najeriya ta amince da kudurin dokar kafa hukumar kula da yankin Arewa Maso-Gabashi.
    Majalisar ta amince da kudurin dokar ne bayan ta yi mata karatu na uku.
    Dokar dai ta tanadi ba da kulawa ta musamman ga yankin na Arewa Maso-Gabas, wanda yaki ya yi wa mummunar illa.
    To sai dai baya ga jihohin na Arewa Maso-Gabas, majalisar ta amince a shigar da karin wasu jihohin Kano da kuma Filato karkashin kulawar hukumar.
    Inda  wasu daga  cikin mambobin majalisar su ma suka bukaci da  a shigar da nasu jihohin irin su Kaduna, Katsina, Jigawa, da  sauransu, amma hakan ya ci tura.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here