Sakataren Kasuwar Shanun Lovanto Ya Karyata Zargin Rashin Tsaro A Kasuwarsu

0
1124

Musa Muhammad  Kutama   daga   Lovanta
\’YAN kasuwar shanu da ke Lovanta, Jihar Abiya sun nuna  takaicin suna bata masu suna da  takwarorin su \’yan kasuwar shanu   shanu ta Okigwe, Jihar Imo suka yi   da kuma kasuwar su abin ya basu mamamki alhali tsawon shekara goma sha biyu suna kasuwancin su tare a Lovanta, tun daga lokacin da suka kaura daga Umuahiya suka dawo Okigwe ,daga nan kuma suka baro okigwe suka  dawo Lovanta sai  wani bangare  na \’yan kasuwar  \’yan Mubi, suka kaurace wa kasuwar suka   koma Okigwe cikin watan jiya sai gashi sun ji wasu daga cikin shugabannin waccan kasuwa shanu ta Okigwe na bata masu suna da kuma sunan kasuwar su.
Alhaji Baba Ahmed , sakataren kasuwar shanu ta Lovanta ne ya bayyana haka  yayin zantawar da  suka yi  da wakilinmu na kudanci  ya ce kasuwar  su tana nan   daram tana ci  kowace rana ta Allah daga Litinin zuwa Lahadi to amma sai gashi abin mamaki wasu \’yan kasuwa \’yan Mubi da suka ware daga cikin mu suka koma Okigwe tsohuwar kasuwa wadda dalilin rashin tsaro da kuma yawaita yi masu fashi ana  kashe  masu mutane \’yan kasuwa ya sanya suka kaurato suka dawo Lovanta amma sai ga shi don sun koma can suke bata sunan mu da kuma na kasuwar mu”inji shi.
Ya ci gaba da cewa “a saboda rashin tsaron  ne ma   a kasuwar shanun ta Okigwe , wata rana 27 ga wata shekara ta 2002 \’yan fashi suka rutsa
Fulani a dakin su suna kirga kudi bayan sun gama cin kasuwa za su yi masu fashi suka yi da dukan kofar dakin su bude ganin cewa mutanen sun ki bude wa barayin kofa ne  sai suka zuba wa dakin fetur suka cinna masa wuta suka gudu take mutane  goma 12 da ke cikin gidan da barayin suka zo fashi suka kone sannan kuma a wani fashi na daban barayin dai suka sake kashe  mutanen mu 8 to amma ka ji don kin gaskiya da son zuciya irin na dan Adam suka ce kasuwar mu ce babu tsaro ai mun zagaya da kai kasuwar ka gani ka ga yadda take ga shanu  nan masu yawa sun haura guda dubu ana sayarwa yanzu ace inda ba tsaro a kawo dukiya ta dimbin nairori ace za a ajiye?.Wannan zargi da suka yi  ba gaskiya ba ne ai akwai jami\’an tsaro kafin ka shiga da kuma in za ka fita Lovanta”.
Sakataren kasuwar shanu Lovanta ya kara da cewa dalilai uku zuwa hudu ne ma ya sanya suka kaurato daga Umuahiya,Jihar Abiya  suka dawo Okigwe Jihar Imo  a watan Afrilu na 1994 “dalilin barin mu umuahiya zamanin mulkin soja ne lokacin gwamnan jihar Ike Nwosu lokacin marigayi Sani Abacha na shugaban kasa gari ne yazo ya matsewa kasuwar kasan babu yadda za,ayi kasuwar dabbobi na cikin gari ganin haka ne fa sai gwamnan na wancan lokaci ya gina mana wata kasuwar a Ubakala ,kuma kasuwar tayi mana daji sosai shine mutanen mu sukace basu so shi kuma ya yi amfani da karfin mulkinsa ya ce sai a koma Ubakala, mutanen mu suka fusata shi ne suka ki aka dawo okigwe, lokacin gwamnan jihar Imo na soja Tanko Zubairu ne sannan shugabar karamar hukumar Okigwe  Rose Amunike ,ce shugabar karamar  hukumar Okigwe aka bamu wuri muka  zauna muke kasuwancin mu “.inji sakatare.
Karshe Alhaji Baba Ahmed sakataren kasuwar shanu ta lovanta ya nemi wadancan abokan huldar su  da suka bandare da su  dawo aci gaba da kasuwanci kamar yadda keyi tsawon shekara goma sha biyu dasu anan Lovanta.Su bar yawo suna bata masu suna da kuma shara masu karya kan abin da ba shi  kenan   ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here