Kasafin Kudin 2017: Za A Fita Daga Matsin Tattalin Arziki Da Ya Dabaibaye Najeriya

0
888

 

Jabiru A Hassan, Daga Kano.

AN bayyana cewa kasafin kudin shekara ta 2017 zai ceto Nijeriya  daga halin matsin tattalin arzikin da take fama da shi idan aka dubi irin tanade-tanaden da gwamnatin tarayya ta yi cikinsa.
Wannan tsokaci ya fito ne daga kungiyar tabbatar da shugabanci nagari a karshen taron da ta gudanar na karshen shekara a Kano, inda kuma ta yi fatar cewa  majalisar  dattawa da ta wakilai za su  gaggauta amincewa da wannan kasafin kudi ta yadda gwamnatin  Tarayya za ta fara aiki da shi ba tare da samun tsaiko ba.
Shugaban kungiyar Alhaji  Bashir Ahmed ya sanar da cewa  alamu sun nuna cewa  nan gaba kadan kasar nan za ta zamo  cikin yanayi mai kyau bisa la\’akari da irin kokarin da shugaban kasa Muhammadu Buhari  ke yi wajen dora  ta a kan dandamali mai inganci kamar sauran kasashen da suka ci gaba a duniya.
Alhaji Bashir  Ahmed ya kuma yi kira ga \’yan Nijeriya da su ci gaba da yi wa wannan gwamnati fatar alheri  domin ta cimma kyawawan manufofin ta na bunkasa kasa.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here