Jam\’iyyar ADP Za Ta Karbi Mulkin Nijeriya Daga APC A Zaben 2019-Nanyah Andrew

    0
    1091
    Isah  Ahmed, JosMISTA Nanyah Andrew Daman shi ne  shugaban riko na sabuwar  jam\’iyyar
    nan ta ADP a jihar Filato kuma shi ne shugaban kamfanin buga mujallar
    nan ta Newsgate da ake bugawa a garin  Jos.

    A wannan tattaunawa da ya yi da wakilinmu ya bayyana shirin da wannan
    sabuwar jam\’iyya ta ADP tayi, na karbe mulkin Nijeriya daga jam\’iyyar
    APC.

    Ga yadda tattaunawar ta kasance

    GTK; Mane ne manufofin wannan sabuwar    jam\’iyya ta ADP?

    Nanyah; Ita dai wannan sabuwar jam\’iyya ta ADP, wadda  wasu masu
    kishin kasa da suka haxa da matasa da waxanda basu taba rike wasu
    mukamai ba ne suka hadu suka kafa ta.

    Kuma babbar manufar wannan jam\’iyya shi ne ceto al\’ummar Nijeriya daga
    irin mawuyacin halin da suke ciki, musamman kan tashi  komai na
    harkokin rayuwa  a Nijeriya.

    Idan wannan sabuwar jam\’iyya ta ADP ta karvi mulkin Nijeriya, zata yi
    amfani da tsarin tattalin arzikin da zai fito damu daga cikin wannan
    mawuyacin hali da muke ciki.

    Kuma a tsarin wannan jam\’iyya muna son mu yi amfani da tsarin zaben
    A4, a dukkan zabubbukan da zamu yi.  Wato tsarin mutum ya tsaya zabe
    mutanen da suke sonsa su layi su bi  bayansa su zabe shi. Babu ruwanmu
    da tsarin  zaben wakilai.

    Idan kana da farin jini a kauyenka ko a  garinka ko a  jihar ka, sai
    ka fito ka tsaya mutane suyi layi, su zabeka. Babu ruwanmu da tsarin a
    kawo wasu mutane wadanda zasu wakilci jama\’a  daga wata karamar hukuma
    ko jiha ko wani gari. Duk \’yan jam\’iyyar nan ne zasu tsaya su zabi
    wanda suke so.

    Haka zamu a zaben shugabannin jam\’iyya da zabubbukan  \’yan takarar mu
    a matakan zaben shugabannin  kananan hukumomi da gwamnonin jihohi da
    \’yan majalisunsu da zaben \’yan majalisun  tarayya da shugaban kasa,
    duk haka zamu yi. Domin muna son mu tsayar da mutanen da jama\’a suke
    so.

    GTK; Maye banbancin wannan sabuwar jam\’iyya ta ADP da jam\’iyyun  PDP da APC?

    Nanyah; Ita dai wannan sabuwar jam\’iyya ta ADP kamar yadda na fada
    wadansu masu kishin kasar nan ne suka hadu suka kafa ta. Kuma wannan
    sabuwar jam\’iyya ta kowa da kowa ce.

    Amma kaga jam\’iyyun PDP da APC jam\’iyyu ne na masu kudi  da wadanda
    suka dade suna rike da mukamai iri daban daban a Nijeriya. Sune  ne
    suka taru suka kafa su, sune shekaranjiya sune jiya sune kuma yau.
    Irin mutanen da  waxannan  jam\’iyyu na PDP da APC ke nan suka kunsa.

    GTK; Kana ganin wannan jam\’iyya zata iya karvar gwamnatin Nijeriya
    daga jam\’iyyar APC?

    Nanyah;  Babu shakka bisa dukkan alamu wannan sabuwar jam\’iyya, zata
    iya qarvar mulkin Nijeriya daga jam\’iyyar APC. Domin Akwai fitattun
    \’yan siyasa da suke son shigowa wannan sabuwar jam\’iyya kamar tsohon
    mataimakin shugaban kasa  Alhaji Atiku Abubakar da  tsohon shugaban
    kasa Olusegun Obasanjo da tsohon Shugaban kasa Janar Babangida da
    tsohon shugaban kasa Abdulsalam Abubakar da gwamnonin jihohi masu ci
    guda 16 da Sanatoci masu ci guda 32 da \’yan majalisar wakilai guda 148
    duk suna nan suna shirin dawowa wannan sabuwar jam\’iyya ta ADP. Don
    haka muna ganin wannan jam\’iyya zata mamaye kasar nan, ta karve mulki
    a zaven shekara ta 2019.

    GTK; Daga lokacin da kuka kawo wannan jam\’iyya nan jihar Filato, zuwa
    yanzu yaya kaga yadda al\’ummar  jihar suka karvi wannan jam\’iyya?

    Nanyah; Daga lokacin da muka kawo wannan jam\’iyya nan jihar Filato
    zuwa yanzu al\’ummar jihar nan sun fito sun rungume ta. A yanzu duk
    inda ka shiga a jihar nan zaka ji ana maganar wannan sabuwar jam\’iyya.

    Domin mutanen jihar nan sun gaji da jam\’iyyun PDP da APC.  Duk
    qanannan hukumomin jihar nan 17 mun riga mun kafa shugabannin riko. A
    ko\’ina a jihar nan ana nan ana ta yin rijistar \’yayan wannan jam\’iyya.

    GTK; Maye zaka ce kan kara lokacin shugabannin kananan hukumomi da
    gwamnan jihar Filato ya yi?

    Nanyah; Abin da yasa gwamna Lalong ya yi wannan karin lokaci na
    watanni 6 ga  shugabannin qananan hukumomi, ya sanya an yi masa
    bincike ne a kananan hukumomin jihar nan 17. Wannan bincike ya nuna
    masa cewa idan ya yi zaben nan a yanzu, da kyar zai iya cin kananan
    hukumomi guda 5. Don haka ya yi wannan karin lokaci  don ya yi wasu
    abubuwan da zasu farantawa jama\’a rai. Amma ina mai tabbatar maka ko
    maye gwamna Lalong  ya yi ba zai sami nasara ba. Domin babu abin da ya
    yiwa jihar nan.

    Maganar biyan albashin da ya yi ba Buhari ne ya bashi kudin biyan
    albashin ba?  Ana bin jihar nan bashi sama da naira biliyan 100 amma
    babu wanda aka baiwa ko kwabo a cikin wadanda suke bin jihar nan
    bashi. Alhalin an yi yarjejeniya da shi cewar wadannan kudade da
    shugaban kasa Buhari ya baiwa gwamnoni kashi 50 su biya albashi kashi
    50 kuma su biya basussuka amma gwamna Lalong bai biya bashin ko kwabo
    a cikin wadannan kudade ba.

    Babu abin da gwamna  Lalong ya yi a jihar nan, sai yawace yawace da
    kashe kudaden jihar nan. Ana daukar hayar jirgi  don  kai \’yarsa
    makaranta a Yola aje a dawo da ita. Alhalin mutane suna mutuwa a
    asibitoci saboda rashin magunguna. Hanyoyi babu gyara don haka muna da
    karvin gwiwar karve gwamnatin jihar Filato daga APC.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here