A Duk Duniya Babu Kasar Da Ta Kai Arewacin Nijeriya Kasar Noma-Dogara Isiyaka

    0
    1274

    Isah Ahmed, Jos

    ALHAJI  Dogara Isiyaka  da ke zaune a garin Jos babban birnin jihar
    Filato, wani tsohon ma\’aikacin gandun daji ne da ya yi shekaru 55 yana
    aikin gandun daji, tun a lokacin mulkin turawa.

    A wannan tattaunawa da ya yi da wakilinmu, ya bayyana cewa a  duk
    duniya babu kasar da ta kai yankin arewacin Nijeriya kasar noma. Ya ce
    amma ana lalata wannan kasar noma a yankin  saboda sare itatuwan da
    ake yi a kullum.

    Ga yadda tattaunawar ta kasance

    GTK; Da farko zamu so muji tarihin rayuwarka

    Dogara Isiyaka; Ni dai sunana Alhaji Dogara Isiyaka kuma ni mutumin
    garin Keffi ne dake jihar Nasarawa. Amma a yau ina da shekara 78 da
    zama a nan garin Jos. Kuma a yanzu ina da shekara 127  da watanni 6, a
    duniya.

    Nayi makarantar elementari kuma nayi aikin gwamnati tun a zamanin
    turawa  a sashin  shuke shuken itatuwa,  har  na tsawon shekara 55.

    Daga nan nace  zan je na huta. Don haka nayi ritaya har ya zuwa wannan
    lokaci da muke ciki. A yanzu  Ina karvar fansho guda biyu daya a
    gwamnatin tarayya, daya kuma a gwamnatin jihar Filato.

    GTK; To, yaya zaka kwatanta mana yadda ake  kula da gandun daji
    ada da kuma wannan lokaci da muke ciki?

    Isiyaka Dogara; Wannan tambaya tana da mahimmanci domin  maganar aikin
    kula da gandun daji a Nijeriya, yanzu komai ya lalace.  Kuma abin da
    ya kawo haka shi ne son zuciya da kuma  rashin sani. Domin idan aka
    bari itatuwa suka qare a kasar nan, za a shiga wata masifa wadda sai
    dai Allah ya kiyaye.

    Domin idan hamada ta mamaye arewacin kasar nan babu wani abu da zamu
    iya yi. Kuma itace yana daya daga cikin abin da yake hana hamada
    mamayar kasar nan.

    A duk duniya babu kasar da ta kai yankin arewacin Nijeriya kasar
    noma. Amma ana son abar wannan kasar noma  ta lalace gabaki daya,
    sakamakon kwararowar hamada saboda sare itatuwan da muke yi a Kullum.

    Ada duk gandun dajin da muke da su a kasar nan, babu wani mutum da ya
    isa yaje ya sari itace ko kuma ya yanki ciyawa a ciki. Amma a yanzu
    abin ba haka yake ba, yanzu ma babu gandun dajin domin ana sare
    itatuwa ta ko\’ina a kasar nan.

    Ada kowanne wuri zaka ga anje an shuka itatuwa don kasa ta zamo
    dausayi mai kyau. Idan akwai itatuwa a  gona, misali  wani yana da
    gona mai fadin eka 200 amma babu itace a
    ciki. Wani kuma yana da gona
    mai fadin  eka 100, amma yana da itatuwa a ciki, to amfanin gonar da
    zai samu  sai ya ninka yawan  wanda yake da gona mai fadin  eka 200
    babu itatuwa a ciki.

    Ada itatuwa suna da dokoki masu karfi, domin idan an ce wannan gandun
    daji ne ba a taba komai a ciki. Ko  futsari mutum ya yi a ciki za a
    iya kama shi. Kuma ada akwai wadannan gandun daji a ko\’ina a kasar
    nan. Domin itatuwa sune lafiyar dan adam da dabbobi. Domin iskar da
    itace yake kawowa yana taimakon dan adam da dabbobi.

    Amma yanzu ana ta sare itatuwa a Nijeriya  kuma ba a dasa wasu. Idan
    muka cigaba da yin haka za a wayi gari babu itatuwa a Nijeriya.

    GTK;; To mene ne mafita kan wannan al\’amari?

    Dogara Isiyaka; Mafita ita ce a koma an sake kafa gandun dazuzzuka a
    kasar nan. A dauki ma\’aikata masu ilmi wadanda za su tafiyar da wannan
    aiki. Idan ba a yi haka ba, nan gaba ko itacen girki ba za a samu ba a
    Nijeriya.

    Saboda haka  gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohin kasar nan su
    koma kan harkokin inganta itatuwa. Domin a raya kasar nan, a sami wajen
    noma. Itatuwa suna da matukar amfani  kan aikin gona. Ko a gida itace
    yana da matukar amfani kwarai da gaske. Domin idan babu itace a gida,
    iska za ta iya kwashe rufin gidan amma idan da itace a gidan itacen zai
    iya tare iskar.

    GTK;; Wanne irin tasiri ne kake ganin kasar nan zata samu idan aka
    rungumi harkokin  itatuwa?

    Isiyaka Dogara; Babu shakka idan muka rungumi harkokin itatuwa a kasar
    nan, za mu sami babban amfani. Domin  itatuwa suna  da matukar
    mahimmanci a ko\’ina a duniya ba a Nijeriya kadai ba. Saboda haka idan
    kaje kasashen turawa zaka ga kowanne babban gari yana cike da itatuwa.
    Domin  itatuwa suna bai wa mutane lafiya kuma suna tsare wasu abubuwa
    a gidajen mutane.  Saboda haka idan aka  dawo da maganar shuka itatuwa
    a Nijeriya za  a sami babban ci gaba.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here