MAJALISAR DATTAWA TA DAURE WA CIN HANCI DA RASHAWA GINDI A NIJERIYA-IMAM USAMA

    0
    1204
    Isah Ahmed, Jos
    IMAM Ibrahim  Awwal [Usama] Funtua shi ne Limamin masallacin unguwar
    \’yan majalisar  tarayya da Ke Zone  B,  Apo a babban birnin tarayya
    Abuja.
    A wannan tattaunawa da ya yi da wakilinmu kan dambarwar da ke faruwa
    tsakanin majalisar dattawa da fadar shugaban Kasa. Kan kin amincewa da
    sunan shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu da majalisar tayi da kuma
    tilastawa shugaban hukumar kwastan ta Kasa Kanar Hameed Ali ya sanya
    kakin hukumar.  Ya bayyana cewa majalisar dattawa ta daurewa cin hanci
    da rashawa gindi a Nijeriya.
    Ga yadda tattaunawar ta kasance
    GTK; Mene ne za ka ce dangane da dambarwar da ke faruwa na kin amincewa
    da shugaban hukumar EFCC Ibarahim Magu da kuma tilasta wa shugaban
    hukumar kwastan ta kasa Kanar Hameed Ali mai  ritaya, sanya kakin
    kwastan da ‘yan majalisar dattawa suka yi?
    Imam Usama; Babban abin da zance kan wannan dambarwa shi ne wani abu
    ne na son zuciya. Saboda idan ka dauki shugaban hukumar EFCC, tun da
    farko shugaban kasa ya tura sunan wannan mutum don ‘yan majalisar
    dattawa su amince amma suka ki.
    Ya zo ya sake tura masu sunan wannan mutum a karo na biyu, domin su
    amince sun sake kin amincewa da wannan mutum. Kuma kafin ‘yan
    majalisar dattawan nan su sake kin amincewa da sunan wannan mutum a
    karo na biyu.  Akwai wani sanata daga cikin su da suka cire shi daga
    kan wani shugabanci da yake rike da shi  a  majalisa, saboda yana
    goyan bayan wannan shugaban hukumar ta EFCC.
    Wannan dambarwa da ake yi a majalisar  kan Ibrahim Magu wasu ne daga
    cikin ‘yan majalisar  saboda laifaffukan da suka aikata suke ganin
    cewa idan Ibrahim Magu ya sami wannan dama ba zai saurara masu ba.
    Wannan dalili shi ne ya kawo wannan dambarwa kan amincewa da shi  a
    majalisar.
    Shi kuma shugaban hukumar kwastan ta kasa Kanar Hameed  Ali mai ritaya
    da majalisar take  maganar cewa dole ne, sai ya sanya kakin hukumar.
    Yanzu wannan magana tana gaban kotu kuma masana  dokokin kasar nan,
    suna ganin cewa babu wata doka da ta  tilasta cewa dole sai ya sanya
    kakin na hukumar ta kwastan.
    Kuma yanzu  majalisar nan tana nan, tana bincike  kan wasu motoci da
    shugaban majalisar ya sayo wadanda aka yi masu takardun kwastan na
    bogi. Haka kuma majalisar tana bincike kan wasu abubuwa da suka shafi
    Sanata Dino Melaye. Kaga wannan ya nuna cewa saboda Hameed Ali bai
    daga masu kafa bane yasa suke wannan abu. Wannan wani babban  abin
    kunya ne ga Sanatoci a ce suna yin wadannan abubuwa don ba a daga masu
    kafa ba.
    Akwai wasu shugabanni a baya wadanda suka yi laifaffuka, amma wadannan
    Sanatoci basu yi ko mai a kai ba. A lokacin gwamnatin da ta gabata
    harin bam na farko a Nijeriya da kungiyar  ‘yan tawayen Neja Delta
    vangaren Herry Okar suka kai a Abuja, kuma suka fito suka ce su ne suka
    aikata. Shugaban kasa na lokacin ya fito ya ce ba su ne suka kai
    wannan hari ba. Shi ya san wadanda suka kai wannan hari. Amma a
    lokacin ‘yan majalisar  ba su cewa shugaban kasar komai ba, kan wannan
    katobara da ya yi.
    Bayan haka ya kara fitowa ya ce ya san ‘yan boko haram yana cin
    abinci da su yana komai tare da su, duk da irin halin da aka shiga a
    wancan lokacin, amma ba su ce komai ba.
    GTK; Ganin irin wannan dambarwa da take faruwa kan wadannan mutane da
    shugaban kasa ya nada, yaya kake ganin dangantakar shugaban kasa da
    majalisar dattawa?
    Imam Usama; Gaskiyar magana idan aka yi la’akari da wadannan abubuwa
    da suke faruwa, dangantakar shugaban kasa da majalisar dattawa bata da
    kyau. Lallai ne shugaban kasa  ya lura da wannan abu ya yi gyare-gyare
    domin  ya sami cimma nasarar da yake son ya cimma. Domin a yau a cikin
    wadannan ‘yan majalisar dattawa da wuya a sami sama da mutum 10 da
    suke tare da shi dari bisa  dari. Sai dai saboda  tsoro wasu ba za su
    iya fitowa fili su bayyana kan su ba.Wadanda kuma suke tare da shi  ba
    a basu dama suyi magana a majalisar. A yanzu a cikin shugabanin wannan
    majalisa akwai wadanda ba dan suna jin tsoron ‘yan Nijeriya ba, zasu
    iya fitowa su ce zasu tsige shugaban  kasa.
    Abin da ya sanya ‘yan majalisar nan suke  yin wadannan abubuwa shi ne
    mafiya yawa daga cikin su akwai tsofaffin gwamnoni, wasu kuma sun
    rike  manyan mukamai kuma suna ganin sun yi wasu laifuffuka. Ta yadda
    idan suka bada dama aka yi doka wadda za ta hukumta kowa to ba za su
    sha ba.
    Don haka yanzu a Nijeriya babu inda aka daure wa cin hanci da rashawa
    gindi kamar a majalisar dattawan Nijeriya. Don haka muna kira ga
    malamai da fastoci su fito su yaKi wannan ta’addanci na cin hanci da
    rashawa da majalisar dattawan  Nijeriya ta Daure wa  gindi.
    GTK; To a ganin ka  wadanne matakai ne ya kamata  shugaban kasa ya
    dauka kan wannan al’amari?
    Imam Usama; Matakan da ya kamata ya dauka sune ya tabbatar da cewa
    kamar yadda aka san shi cewa shi adali ne. To ya tabbatar da cewa duk
    kasar nan babu wanda yafi karfin a hukumta shi. Idan har wadanda suka
    yi shugabancin kasar nan, za su iya laifi a kamasu a kai su gidan yari.
    A yanzu banga wani da  ya wuce a hukumta shi  ba, a qasar nan.
    Amma ace wasu sun fi karfin hukumci a cikin wannan gwamnati wannan shi
    ne matsalar. Don haka ko dan da shugaban kasa ya haifa, idan ya
    tabbatar mabarnaci ne ya raba shi da matsayin da ya bashi kuma ya
    tabbatar an hukumta shi.
    Mataki na biyu shi ne duk ma’aikatar da ya san wasu abubuwa suna
    faruwa sunki ci sunki cinyewa ya yi kokari ya nemo wadanda suka rike
    wannan ma’aikata a baya,  ya nemi shawararsu. Idan ya zama mai karbar
    shawara in Allah ya yarda za a sami nasara.
    GTK; Karshe wanne sako ko kira ne kake da shi zuwa ga al’ummarNijeriya?
    Imam Usama; Sakona ga ‘yan Nijeriya shi ne ya kamata su sani cewa ba
    zai  yiwuwa  su zuba ido suna kallo ana yin bubuwa marasa kyau a
    Nijeriya ba. Bai kamata a zubawa shugaban kasa  ido shi kadai ace shi
    ne zai gyara komai a Nijeriya ba. Dole a fito a tallafa masa kan gyara
    abubuwan da suka lalace a Nijeriya.
    Kuma maganar da shugaban kasa yake yi cewa shi yana bin doka da oda
    ne. To ya kamata ya sani cewa a Nijeriya akwai dokar da idan  ka
    karyata, ya kamata a yi maka kyauta, kan karya wannan doka da ka yi.
    Yanzu yadda abubuwa suka lalace a Nijeriya babu yadda  za a yi a ce za a
    bi doka dari bisa  dari. Dole sai an karya wata dokar sannan za a iya
    yin wani gyaran.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here