An Yi Jana’izar Sheikh Alhassan Sa\’eed Adam Jos Yau A Kano

0
1464

Isah Ahmed, Jos Da Usman Naasidi Daga Kaduna

A yau ne dubban daruruwan mutane suka yi jana\’izar fitaccen malamin addinin musuluncin nan da ke zaune a

garin Jos, kuma jigo a kungiyar Jama\’atu Izalatil Bad\’ah Wa\’ikamatis sunnah ta kasa Sheikh Alhassan Sa\’eed Adam Jos bayan da Allah Ya karbi rayuwarsa jiya Laraba da yamma.

Shi dai marigayi Sheikh Alhassan Sa\’eed Adam Jos ya rasu ne  a wani asibiti a Kano bayan da ya je don a duba lafiyarsa a wannan rana ta Laraba.

Ya rasu ya bar matan aure 4 da  \’yaya maza da mata  26  da jikoki da dama.

An haife marigayin  a garin Mikeke da ke karamar hukumar Gumel a jihar Jigawa shekaru 59 da suka gabata.

Ya yi karatu a jami\’ar Madina da jami\’ar Usman Danfodio da ke Sakkwato da jami\’ar Jos.

Kafin rasuwarsa shi ne na\’ibin babban  malami  mai tafsirin watan azumin Ramadan a masallacin sultan Bello da ke Kaduna.  Har\’ila yau kuma shi ne  shugaban fatawa na kungiyar Jama\’atu Nasril Islam  reshen Jihar Filato.

 

Top of Form

Bottom of Form

Top of Form

Bottom of Form

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here