AN SAMAR DA TABBATACCEN TSARO A KUDANCIN KADUNA – Hafsan Tsaro

0
770
Daga Usman Nasidi
BABBAN hafsan tsaro na kasa (CDS), Janar Abayomi Olanisakin, a ranar Talata, 26 ga watan Afrilu ya ce, sojoji na musamman na samar da tabbataccen sakamako a harakar tsaro a yankin kudancin Kaduna.
Hafsan tsaron ya shaida wa manema labarai a Kaduna cewa `Operation Harbin Kunama ll, da aka kaddamar da mako daya da ta gabata ta kwace makamai daban-daban a yankin.
CDS ya ce sojojin na amfani da hanyoyin magance batun rashin tsaro a yankin ciki har da fashi da kuma barayin shanu.
A cewar shi, shugabannin gargajiya, addinai da kuma siyasa duk suna da hannu a cikin kokarin ganin cewa an tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Hafsan tsaron ya bayyana hakan ne a garin Kaduna yayin kaddamar da wata dakin taron mai mutane 1,000 a kwalejin kimiya na sojojin sama wato ‘Air Force Institute of Technology’.
Ya yaba wa babban hafsan sojan sama, Air Marshall Sadiq Abubakar domin hangen nesa da kuma abar koyi shugabanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here