ADURGUZA.

0
1382

WASU matasa ne su biyu dayan ana kiransa  Ci-wake  dayan kuma ana kiransa Adurguza , dukan su mashaya giya ne sun sha giya sun bugu sai dayan yana waka yana cewa Yesu na gabanmu yana bayanmu sai ya zo zai tsallaka titi sai Ci-wake ya ce Adurguza kar ka tsallaka-kar ka tsallaka ya kara cewa kar ka tsallaka –karka tsallaka .Sai Adurguza ya bi ya tsallaka titi sai mota ta buge shi sai Jonah  ya ce wa wannan direba da ya kade Adurguza ya ce ka bi ka tafi abinka kurum sai direba ya tafi.

Sai ga ‘yan sanda suka zo suna dubawa sai Jonah  ya zo ya fada wa ‘yan sanda yadda abin ya faru ya ce Adurguza ne ya taho yana waka yana cewa Yesu na gabanmu yana bayanmu sai mota ta bi ta durguje shi sai ya ce wa ‘yan sanda amma na bi na dauki lambar motar ‘yan sanda suka ce to mece ce lambar motar? Sai  ya ce fi el [PL] amma sauran iska ta bi ta share sauran.

Daga  Hashimu  Hassan

Layin Bagobiri Kalaba

08096176141

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here