Cin Hanci: Babu Tantama Buhari Alheri Ne Ga \’Yan Kasar Najeriya

    0
    709
    ​Muhammad Sani Chinade, DAGA DAMATURU
    WANI hanshakin dan kasuwa Alhaji Gambo mai citta da ke babbar kasuwar
    Potiskum a Jihar Yobe ya bayyana cewar, yaki da cin hanci da rashawa
    da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ke yi don kai kasar nan ga
    tudun tsira tunin an kai ga nasarar wannan fafutuka.
    Alhaji Gambo mai citta ya bayyana hakan ne a tattaunawarsu da GTK a
    garin Potiskum dangane da ce-ce-ku-cen da wasu ke yi na babu abin da
    wannan gwamnati ke tabukawa.
    Ya kara da cewar, wannan yaki da cin hanci da rashawa da shugaba
    Buhari ya dukufa don yi ai ba ga kowa ya taimaka ba illa ga mu \’yan
    kasa.
    Shi ya sa ma akullum muke masa addu\’ar Allah (SWT) Ya taimake shi bisa
    ga wannan kudiri nasa wadanda kuma suke masa zagon kasa kan wannan
    tsarkakakken aiki nasa na yaki da almundahana  to su saurari
    sakamakonsu
    daga Allah (SWT) domin ba masu kaunar kasar nan bane.
    Ya kamata al\’ummar kasa su sani cewar, wannan aiki da gwamnatin
    Muhammadu Buhari ke yi ta na yi ne ba wai don amfanin yanzu kawai bane
    aiki ne da zai amfani kasa har illa masha Allahu matukar an kai ga kakkabe dukannin
    bara-gurbi domin ai yanayi ne don ceto tattalin arzikin kasa da kuma al\’ummarta.
    Kuma ma ai ayyukan da Muhammadu Buhari ke yi kan abin da ya shafi yaki
    da almundahana ayyuka ne da ya kyautu  dukannin \’yan kasa mu tsaya mu
    yi masa godiya tare da addu\’ar Allah madaukakin Sarki ya kara kare shi tare da
    bashi karfin gwiwar ci gaba da sauke nauyin al\’ummar da ya dauka.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here