\’Yan Sanda Sun Kama Wata Mata Da Ke Yi Wa \’Yarta Kawalci A Kuros Riba

0
926

MUSA MUHAMMAD KUTAMA, Daga Kalaba

‘YAN sanda a Jihar Kuros Riba sun cafke wata mata mai suna Udoaka Sunday  tare da wasu mutum uku da ake zargi da cin zarafin ‘yarta  mai shekara 12 da haihuwa da take gayyato maza suna yin lalata da ‘yarta tana karbar kudi gurin su da kuma  duk namijin da ta samu zai yi  lalata da ‘yarta ta kama daga naira dubu 15.zuwa abin da ya fi haka gurin samarin yarinyar .

Wani makwabcin matar Udoaka  ya  bayyana wa wakilinmu na kudanci  a sirrance cewa”ba ta dade da karbo naira dubu 15 ba  wurin wani tsohon soja mai suna   Effiom Okon, da ma wasu mutum hudu duk a zatonta ba a san abin da take yi ba tana bin samari da masu abin hannu tana karbar kudi hannun su tana hada su da ‘yarta suna lalata da ita”.

Majiyar labarin wannan jarida, ta ci gaba da cewa haka Udoaka take bin mutane musamman wadanda suke karbar kudin fensho tana karbe masu kudi tana tura ‘yar wurin su kuma ba tun yanzu take yin haka ba ta  dade tana yi takan gargadi ‘yar da kada ta rika fashin zuwa wurin mutanen tana biya musu bukatar su.

Wakilinmu ya tambayi mahaifiyar yarinyar Udoaka Sunday yadda aka yi har aka fasa kwai sai ta ce “ Yarinyar ce da ta ga abin ya isheta sai ta gaya wa malamin su na makarantar boko ,shi kuma malamin ya sanar wa kungiyar kare cin zarafin yara kanana daga nan kuma suka sanar wa ‘yan sanda kwatsam ina zaune gida suka zo suka tafi da ni”inji ta.

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan Kuros Riba  Irene Ugbo, ta tabbatar mana da labarin kana  kuma ta ce tsohon soja Effiom Okon, da uwar yarinyar   Udoaka Sunday, suna nan hannun su ana tsare da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here