Ta Kafa Shugabannin Riko Su Uku

    0
    928

    Muhammad Sani  Chinade, Daga Damaturu

     

     

    KUNGIYAR teloli ta kasa reshen Jahar Yobe ta kaddamar da kwamitin

    mutane 3 da za su rike harkokin kungiyar a matsayin riko na tsawon

    lokacin da ba a ambata ba kafin gudanar da babban zabenta  don ciyar

    da kungiyar gaba.

    Da yake jawabi ga GTK bayan da aka kaddamar da su a garin

    Damaturu sabon shugaban rikon, Alhaji Ahmad Alhaji Modu ya ce, sun hada

    wannan taro ne da zimmar hada kan mambobin kungiyar da yawansu ya

    haura mutane dubu 10 a dukannin kananan hukumomin jahar 17 wadda sai

    da hadin kai ne za su iya cimma muradinsu na ciyar da kungiyar gaba.

    Shugaban rikon ya ci gaba da cewar, su masu gudanar da sana\’ar dinki

    wato teloli sun gano cewar, babu yadda za su iya ci gaba ba tare sun

    hada kansu ba  kana su kuma samar da shugabanci nagari ta hanyar kungiya.

    Ya kara da cewar, a fahimtarsu a halin da ake ciki babu yadda za a yi

    masu sana\’a su samu tallafi daga gwamnati ko kuma wasu kungiyoyin ba da

    tallafi ga masu sana\’a na cikin gida da na waje ba tare da kungiya ba.

    Alhaji Ahmad Modu ya kara da cewar, a halin da ake ciki mambobin

    kungiyarsu ta telolin Jahar Yobe ta zabe su, su uku a matsayin

    shugabannin rikon da za su gudanar da harkokin kungiyar kafin gudanar

    da zabe, wato an zabe shi a matsayin shugaban riko sai kuma matsayin

    sakatare an bayar ga Malam Gana Katarko sai kuma matsayin ma\’ajin kudi

    aka bayar ga Musa Ahmad Potiskum.

    Don haka shugaban rikon ya roki gwamnatin Jahar Yobe da ta tallafa

    musu da karin kekunan dinki irin na zamani ko da ma bashi ne ganin

    cewar kungiyarsu ta teloli kungiya ce da ke sahun gaba ta bangaren

    samar wa da matasa aikin yi. Domin in da za a kiyasta kungiyarsu akalla

    takan iya yaye matasa masu koyon sana\’a sama da dari 4 a duk shekara.

    Daga nan sai ya nemi mambobin wannan kungiya ta su da su zama masu ba

    su goyon baya don ganin sun tafiyar da jagorancin da suka dora musu

    bil-hakki da gaskiya don cimma kudirin da suke bukata na inganta

    kungiyar da rayuwar membobinsu.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here