MATUKAR JAMA\’ATA SUN SAKE NEMA NA DON WAKILTARSU A MAJALISAR KASA A SHIRYE NAKE DA IN AMSA….

    0
    757
    Muhammad Sani Chinade, DAGA DAMATURU
    TSOHON dan majalisar dattawan kasar nan mai wakiltar kudancin Jihar
    Yobe a majalisa ta 7 da ta shude Sanata Alkali Abdulkadir Jajere ya
    bayyana kudirin na amsa kiran al\’ummar matukar sun sake nemansa don
    wakiltarsu a majalisa ta 9 mai zuwa a zaben da ke tafe a shekarar 2019.
    Dan majalisar dattawan ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da
    wakilinmu a garin Damaturu dangane da
    yadda yake ga ake tafiyar da shugabancin majalisa ta 8 a karkashin
    shugabancin Abubakar Bukola Saraki.
    Alkali Abdulkadir Jajere  ya ci gaba da cewar yadda yake ganin a
    halin yanzu ake gudanar da shugabancin majalisa ta 8 abin a yaba ne
    musamman in an yi la\’akari da cewar jam\’iyyarsu ta APC ita ce ke da
    rinjaye a majalisar sabanin a majalisar da ya taka rawa cikinta daga
    shekarar 2011 zuwa shekara ta 2015 wato majalisa ta 7 wacce a wancan
    lokacin jam\’iyyar PDP ce ke jagorantar ta.
    Sanata Jajere ya ci gaba da cewar, in an lura majalisar dattawan kasar
    nan da kuma \’yan uwansu na wakilai suna ayyukansu daidai wa daida ta
    yadda suke kokarin samar da dokokin ciyar da kasa gaba kamar yadda
    jajirtaccen shugaban kasarmu Muhammadu Buhari ke da shi. Illa \’yan
    kurakure \’yan kalilan da ba a rasa ba wadanda muke fatan za su gyara
    yadda zai zo daidai da bukatun talakawan kasar nan da su ne suka yi
    tsayuwar daka da ya yi sanadiyyar zuwan wannan gwamnati mai adalci cikin
    ikon Allah.
    Dangane da na\’amta don sake tsayawa takarar kujerar dan majalisar
    dattawa a mazabar kudancin Yobe in har al\’ummarsa sun neme shi a kan
    hakan. Jajere ya ce lalle a shirye yake da ya amsa kiran jama\’ar
    matukar sun neme shi kan hakan domin ai na ji dadi shi ne gari ba na
    saba ba.
    Jajere ya ci gaba da cewar, shi ya hakkake cewar a halin da ake ciki
    al\’ummar mazabar sun gane cewar lalle lokacin da yake wakiltarsu a
    majalisa ta 7 sun samu wakilci nagari sabanin yadda suke a yanzu.
    Don haka ya ba da tabbaci ga al\’ummar mazabarsa kan cewar, a shirye yak
     da ya sake tsayawa don wakiltarsu matukar sun bukace shi a kan hakan.
    Alkali Jajere ya kuma yaba wa Gwamna Ibrahim Gaidam na Yobe dangane da
    yadda yake gudanar da ayyukansa bil-hakki da gaskiya musamman dangane
    da ayyukan raya kasa da yake aiwatar a dukannin sassan jihar.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here