RIKICIN BOKO-HARAM YA HADDASA DUKKAN TABARBAREWAR AL\’AMURA

    0
    1077
    Muhammad Sani Chinade, DAGA DAMATURU
    A wata tattaunawa ta musamman da GTK ta yi da shugaban hadakar
    \’yan kasuwa na karamar hukumar Damaturu cikin Jihar Yobe Alhaji Garba
    Bazam akwanakin baya.
    shugaban ya bayyana irin halin da mambobin kungiyar suka shiga na
    sukurkucewar harkokin kasuwancinsu sakamakon tabarbarewar harkokin
    tsaro da yankinsu ya yi fama da shi da yadda gwamnatin jahar ta yi ta
    kokarin dafa musu don fita daga wannan halin kunci. Asha karatu
    lafiya.
    GTK:- Yaya tarihin wannan kungiya ta ku yake da kuma adadin mambobin ku?
    Bazam:- To ita wannan hadakar kungiya ta mu ta hadakar \’yan kasuwar
    garin Damaturu mun kafa ta ne fiye da shekaru goma da suka gabata.
    Kuma a yanzu haka muna da akalla mambobi fiye da dubu 10 wadanda suke
    cikin kudinmu.
    GTK:- Mambobin kungiyar nan ta ku ta \’yan kasuwar garin Damaturu
    sun hadu da iftila\’i iri-iri a \’yan shekarun nan a dalilin
    tabarbarewar harkokin tsaro ko yaya abin yake ne?
    Bazam:- Lalle kan mambobin wannan kungiya ta mu sun hadu da iftila\’i
    daga Allah SWT kashi dabam-dabam tun daga abin da ya kama ga konewar
    dukiya sanadiyyar tashin gobara ya zuwa konewar dukiya sakamakon
    hare-haren \’yan bindiga da ya kai ga asarar rayuka da dukiyar milyoyin
    Nairori. Da kuma karayar tattalin arziki da wannan lamari ya haifar wa
    aksarin \’yan kasuwar.
    Har ila yau wannan iftila\’i na tabarbarewar harkokin tsaro ya haifar
    da mummunan koma baya ga harkokin kasuwancin wannan yanki namu ta
    yadda za ka tarar a \’yan shekarun baya mutum daya kan sauke kaya fiye
    da tirela 3 a duk sati amma sai da ta kai da lamura suka yi tsamari da
    kyar za ka sayar da buhuna 10 kacal a sati. To ai kaga mun ga iftila\’i
    iri-iri.
    GTK:- To yanzu fa yaya abin yake in ka kwatanta shi da kamar shekaru
    uku da suka shude?
    Bazam:- A hakikanin gaskiya yanzu kan alhamdulilah da yake an samu
    yanayin tsaro ya kyautatu matuka kuma aksarin mutanen da suka
    bar garin tunin sun dawo.
    GTK:- Ko akwai wani tallafi da gwamnatin Jihar Yobe ta baku sakamakon
    wannan iftila\’i iri-iri da ka ce ya fada wa mambobinku?
    Bazam:- Alal hakika gwamnatin jahar Yobe karkashin mai girma gwamna
    Alhaji Ibrahim Gaidam ta yi matukar tallafa wa mambobin mu domin kuwa
    akwai lokacin da aka yi gobaraa cikin babbar tashar motar Damaturu
    yadda mambobinmu suka yi asarar shagunansu da dukiyoyinsu amma da
    Gwamnan ya zo ya gani sai ya bada umarni da a kiyasta asarar da kowane
    dan kasuwa ya yi, da muka yi kiyasi muka kai ma sa cikin kwanaki hudu
    kacal ya amince da a biya mu kashi dari bisa dari na dukkanin kiyasin
    da aka kai masa yadda ya umarci hukumar kai daukin gaggawa ta jahar
    SEMA da ta ba mu Naira Miliyan18 don rarraba wa ga \’yan kasuwar da suka
    yi asarar dukiyoyinsu.
    Haka nan a wancan lokacin ma da mambobin mu suka hadu da iftila\’in
    hare-haren 1` ga watan Disambar 2014 yadda shaguna kusan 78 suka kone
    bayan da gwamna ya zo ya gani da idonsa tare da jajanta wa da kuma
    wasu wurare akalla 5 da suka hadu da gobara nan ma gwamnan bai yi kasa
    a gwiwa ba ya amince da bamu tallafin kudade sama da Naira Miliyamn 60
    don rarraba wa wadanda suka samu kan su cikin wannan iftila\’i.
    Don haka babu abin da zamu cewa gwamnatin jahar ta Yobe da gwamna
    Ibrahim Gaidam sai dai fatan alheri domin kuwa alama ce mai nuna kan
    cewar lalle gwamnan na tare da jama\’arsa kana yana kuma tausa wa musu.
    GTK:- Ko bayan haka kuna da wani koke ko korafi ga gwamnatin jaha
    da kuma ta tarayya dangane da wasu bukatunku?
    Bazam:- Ba shakka lalle shi da baya gajiya da kuka ga mahaifinsa duk
    irin taimakon da ya ba shi hakika kungiyar mu tana sake neman taimako
    daga gwamnatin jahar Yobe dangane da bada jari ga \’yan kasuwar da suka
    karye sanadiyyar tabarbarewar tsaron da yankin ya yi fama da shi
    kasancewar aksarin \’yan kasuwa rashin ishasshen jari na ci musu tuwo a
    kwarya, kuma jarin ko da rance ne da ba shi da ruwa mai yawa
    muna bukatarsa.
    Haka nan gwamnatin tarayya ma muna rokon ta da ta kawo mana dauki ko
    da yake ma dama muna tsammanin hakan daga sabon shugaban mu mai adalci
    Muhammadu Buhari kasancewar a kullum tun daga hawansa karagar mulki ya
    ke bayanin cewar zai mayar da aksarin akalarsa ga wannan yanki namu
    kuma ko yanzu mun gani a kasa tunda tunin ya mayar karfin tsaron kasa
    ga wannan yanki namu don kokarin dawo mana da yanayin tsaro mai
    inganci.
    GTK:- Allah ya taimaka.
    Bazam:- Madallah na gode Allah ya albarakaci wannan jarida tamu mai
    dadadden tarihi wato GTK.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here