JIGO A JAM\’IYYAR PRP YA BUKACI BANGAREN SHARI\’A DA YA DAIDAITA SAHUNSA

    0
    783
    Muhammad Sani Chinade, DAGA DAMATURU
    TSOHON shugaban rusasshiyar jam\’iyyar PRP Halifan marigayi Malam Aminu
    Kano kuma daya daga cikin \’yan kwamitin gyaran kundin tsarin mulkin
    kasar nan Galadiman Damaturu Alhaji Hassan Yusuf ya bukaci bangaren
    shari\’a da  alkalan kasar nan da su yi kokarin daidaita sahu a bangaren
    na shari\’a don dawo da martabar sashin.
    Tsohon mamban kwamitin gyare-gyaren tsarin mulkin  ya bayyana hakan ne
    ga GTK a garin Damaturu dangane da yadda alkalan suke yanke hukunci a
    kotunan sauraren kararrakin zabe mabanbantan hukunce-hukunce bisa
    kararrakin da aka rika kaiwa gabansu da sauran kararrakin da al\’ummomi
    ke kaiwa.
    Galadiman ya ci gaba da cewar, lokaci ya yi da bangaren shari\’ar kasar
    nan zai dawo da martabarsa ta yadda masu shari\’a za su rika yin
    tsayuwar daka don ganin suna yanke hukunci kamar yadda yake a kundin
    tsarin mulkin shari\’ar kasa ba tare da kawo rudani ba.
    Ya ci gaba da cewar, kamar yadda wasu alkalai suka rika yanke hukuncin
    shari\’ar kararrakin zabe abin akwai rudarwa matuka don wasu alkalai
    sukan ce amfani da na\’urar nan ta tantance masu kada kuri\’a wato (card
    reader) ba ta cikin doka amma kuma wasu alkalan kuma suka ce ai amfani
    da wannan na\’ura na da matukar muhimmanci ga dokokin hukumar zabe na
    kasa da ke da nauyin shirya zabukan da ake kalubalantar nasarorinsu
    gaban kotunan.To ai ka ga anan lamuran shari\’ar na da matukar sarkakkiyj
    Alhaji Hassan Yusuf ya ci gaba da cewar, duk da cewar lamarin shari\’a
    ya kunshi abu uku. Wato da farko akwai masu shari\’ar kansu na biyu
    kuma akwai masu kara na uku kuma akwai mu \’yan kallo to amma su masu
    suke da muhimmanci fiye da dukannin bangarorin biyu, don haka ya zama
    wajibi bangaren na shari\’a da ya hada da alkalai da lauyoyi su yi abin
    da ya dace don kauce wa ire-iren abubuwan da suka faru a baya musamman
    dangane da sharu\’un zabe yadda a baya hukunce-hukuncen da alkalai suka
    rika yi ke cin karo da junansu kamar yadda ya rika faruwa lokacin
    zaben marigayi Abiola ta yadda wata kotun Legas za ta yanke hukunci
    wata kotun kuma a Abuja ta yi nata hukuncin da ya sha banban da na waccar
    kotun alhali a kan abu guda ne.
    Dangane da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta yanke a kan
    zaben gwamnan Taraba da kotun ta ce ta ba da nasarar ga \’yar takarar
    jam\’iyyar APC saboda shi gwamnan da ya fito daga jam\’iyyar PDP bai
    shiga zaben share fage ba ai ka ga hakan ya yi daidai tun da yake ai
    doka ta ce in baka shiga zaben share fage ba amma kuma ka tsaya takarar
    babban zabe duk kuri\’un da aka jefa maka tamfar babu ne. To ai ka ga
    wannan hukunci na kotu da ta yi ya yi daidai.
    To amma da yake ita dokar kotu da dokar kasa kowa na mata fassarar da
    ya ga dama ne akwai a karshe sai ga kotun koli ta ba da nasara ga Gwamna
    mai ci na jam\’iyyai adawa ta PDP.
    Don haka ne Galadiman na Damaturu sai ya shawarci alkalai da su rika
    shirya tarukan bita don kara fahimtar juna a tsakaninsu tare da bitar
    shari\’un baya don kokarin tsayar da gaskiya da adalci a shari\’u ganin
    cewar a halin yanzu canji ya wanzu a kasa.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here