AN KAMA ‘YAN SANDA UKU A DELTA BISA ZARGIN KASHE WANI MUTUM

0
809

MUSA MUHAMMAD KUTAMA,  Daga Kalaba

KWAMISHINAN ’yan sandan Jihar Delta  Zanna Ibrahim, ,ya sanar da kama

wasu jami’an‘yan sandan kwanu da ake yi da laifin kashe direban wata

mota mai suna Ejovwokereoghare, kusa da kauyen Emede, na jihar.

,Yan sandan uku suna aiki ai runduna ta 33 da ke Ado Ekiti , Jihar

Ekiti.Kwamishinan ‘yan sandan Ibrahim ya boye wa manema labarai sunayen

‘yan sandan moba da suka yi kisan kan amma ya ce “za a kai su kotu a kan

zargin sun yi kisan kai da kuma nuna rashn kwarewar aiki”.

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Delta ya ci gaba da bayar da bayanin cewa

“’yan sandan suna aikin rakiyar wani daraktan kamfanin Jonesco mai

suna Arigbogha  Johnny, kan titin  filin jirgin sama da ke garin Warri

a lokacin ne suka yi kisan da ake zargin su da aikatawa”.

Ya kara da cewa wata mace da ke gefen hanya mai suna Agwere Hannahta ce

ta sanar wa da ofishin ‘yan sanda cewar “suna tare da wanda suka

kashen a gefen hanya, ‘yan sandan sun zo wucewa a wata mota kirar Hilux

mai lamba  PF 297 SPY, lokacin su kuma sun dawo daga wurin biki kauyen

Emeden  ,ita dai matar ta samu raunuka sakamakon harbi da aka yi musu

Yayin da shi kuma harsashi ya yi masa  jina-jina aka kwashe su zuwa

babban asibitin Olomoro, nan ne likitoci suka tabbatar musu mutumin ya

mutu” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here