AN KUBUTAR DA FASINJOJIN DA AKA YI GARKUWA DA SU KWANAN BAYA A FATAKWAL

0
713

MUSA MUHAMMAD KUTAMA, Daga Kalaba

RUNDUNAR ‘yan sandan Jihar Ribas ta sanar da kubutar da daukacin

fasinjojin motar nan 14 da wasu ‘yan bindiga suka kama suka yi garkuwa

da su kwanan baya a mahadar babbar hanyar east- west da ke mararrabar

Ndele.

DSP  Nnamdi Omoni kakakin rundunar ne ya sanar da haka ga GTK, inda

ya ce “bisa umarnin kwamishinan ‘yan sandan Ribas kwararru kan harkokin

ceto rayukan jama’a na rundunar ne aka baza su, kuma suka yi katarin ceto

su fasinjojin goma sha hudu.” Haka nan kuma rundunar ta gode wa kokari

da hadin kai na al’ummar da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da mutanen

suka bayar har aka cimma nasarar kubutar da su.

Dagan an jami’in ‘yan sandan ya kara da cewa ina mai tabatar muku duka

mutanen 14 an kubutar da su da rayukansu babu wani wanda ya mutu ko

ya yi kwarzane..Idan ba a mance ba ranar wata Litinin ce wasu mahara

suka yi wa motar fasinja kwanton bauna a mahadar Ndele suka kwace motar

da fasinjojin ciki zuwa wata maboya .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here