YA KASHE KANSA DALILIN SAUYIN AIKI ZUWA BORNO

0
778

MUSA MUHAMMAD KUTAMA, Daga Kalaba

WANI jami’in ’yan sanda da ke aiki a rundunar ‘yan sandan Jihar Ebonyi

mai suna  Donatus Oyibe,ya fada rijiya ya kashe kansa a wata mahadar

hanyar  Ukwuakpu  zuwa  Abakaliki.Jihar Ebonyi.Dan sandan wanda asali

dan kauyen Oyibe ne yankin  Ndiagu Ishieke, da ke karamar hukumar

Ebonyi.

Bayanai da wakilinmu na kudanci ya samo daga makusantan dan sandan

sun yi nuni da cewa Donatus Oyibe ya fada rijiya ce saboda an yi masa

sauyin wurin aiki daga jihar zuwa Borno shi kuma ya yanke shawarar mai

makon ya tafi bayan da takardar sauyin wurin aikin ta fito masa a

watan jiya sai ya tafi rijiya kamar zai debi ruwa daga nan sai kawai

ya yanke shawarar fadawa ciki mutane da suka zo wurin dibar ruwa suka

ga abu kamar almara ya fada cikin rijiyar inji majiyar.

Babbar ‘yar mamacin mai suna Ukamaka ta shaida wa manema labarai

cewar “babana ya dauki bokiti ya ce zai tafi rijiya dibar ruwa yana

zuwa tun da ya fita bai dawo ba har tsawon wani lokaci ba mu ga ya dawo

ba shi ne sai suka bi sawu zuwa rijiyar ko da suka isa wajen sun

tarar da bokitin da ya je da shi waje daya a bakin rijiyar amma shi ba su

gan shi ba shi ne da suka leka cikin rijiyar suka gan shi ya taso kan

ruwa ya riga ya mutu”inji ,yar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda ta Jihar Ebonyi  Loveth Ogah

ta boye sirrin afkuwar lamarin amma ta ce nan gaba za ta yi magana da

zarar sun samu tabbacin hakan.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here