Sun Bai Wa Gwamnatin Kuros Riba Tabbacin Dorewar Zaman Lafiya A Jihar

    0
    1319

    MUSA MUHAMMAD KUTAMA, Daga  Kalaba

    SHUGABAN  kwamitin tsaro hadin kai da kuma zama lafiya a Kuros Riba a

    turance PSU&P. Alhaji Ya’u Isma’il Girei ya bayar da tabbacin

    kwamitinsa zai zage damtse domin ganin matasan Kuros Riba musamman

    ‘ya’yan ‘yan arewa mazauna jihar kwata ba su shiga harkoki da za su rika

    zubar da mutuncinsu da na iyayensu a duk fadin jihar.

    Alhaji Isma’il Gorei ya furta haka ne a jawabin marhabun lale da ya yi

    lokacin da wakilan kwamishinan ma’aikatar matasa da wasanni ta jihar

    karkashin jagorancin babban darakta a ma’aikatar Mista Emmanuel

    B.Ekpenyong da mataimakiyarsa uwargida Immaculata E. Ekpenyong suka

    kawo wa kwamitin ziyarar gani da ido a ofishin kwamitin da ke layin

    Bagobiri,Unguwar Hausawa da ke Kalaba fadar gwamnatin jihar.

    Haka nan kuma shugaban PSU&P ya ci gaba da cewa “mun kafa wannan

    kwamiti ne domin tarbiyartar da ‘ya’yanmu da nufin hana su shiga

    nau’o’in tsageranci, kungiyanci da makamantan duk wani aiki da zai

    haddasa husuma da kuma mu hada hannu da gwamnatin jiha da ta tarayya

    wajen bayar da gudunmawa wajen tsaro saboda larura ce ba ta gwamnatin

    jiha ko tarayya ba, a’a sai domin magance kalubalen tabarbarewar tsaro

    da galibi ya zama ruwan dare a duniya”.inji shi.

    Alhaji Ya’u Girei ya kuma bayyana gamsuwarsa matuka gaya yadda ya lura

    matasa da suke zuwa daga jihohin arewacin rani suka rungumi sana’a.

    Ya ce “ Ina matukar farin ciki musamman ma idan na ga ‘yan uwanmu ‘ya’yan

    mu matasa da suke zuwa cin rani suna neman arziki ba su shiga harkokin

    kungiyoyi da kuma harkoki na shaye-shaye domin za mu ci gaba da daukar

    mataki na ganin mun dakile duk wata harka ta shaye-shaye da masu zuwa

    suna bata mana unguwa”.Daga nan ya gargadi matasa da su guji sayen

    kayan sata da kuma saye da sayar da kayan maye domin duk wani wanda

    aka kama zai dandana kudarsa. Idan an samu mutum da laifi babu ruwan

    kwamaitinsa da shi .

    A jawabin nasa shugaban ya karkare da yi wa duk masu neman haddasa

    husuma da sunan raba kasa cewa kowa ya yi hakuri tun da Allah ya hada mu

    kasa daya muzauna tare fitina ba ta da wani amfani kowa ya yi kokarin

    zama mutumin kirki shi ya fi.

    Da yake mayar da jawabi, jagoran tawagar Mista Emmanuel Effiong a

    madadin kwamishinan cewa ya yi “a gaskiya mun gamsu da yadda muka zo

    muka ga ashe hadda shugabann addini da sarakuna jagoran wannan kwamiti

    mun ga ashe akwai liman da sarki a ciki ai dama tun da sakataren wannan

    kwamiti Alhaji Sha’aban Abdullahi ya zo neman izinin gwamnati ta yi wa

    wannan kwamiti rajista muka ce babu wata damuwa, muka ji rajistar da za ta

    kai shekara biyu kafin ta kare a sake sabuntata ganin wadannan manyan

    mutane masu kima da mutunci da muka gani mun san babu wata

    tababa”.inji shi.

    Har wa yau kwamishinan ya kara da cewa “ mun ji dadin yadda kuka shigo

    domin taya mu bayar da gudunmawa wajen harkar tsaro ai mu dama Jihar

    Kuros Riba jiha ce ta zaman lafiya, ba kuma za mu taba bari wani ya zo

    daga wata jiha ko yanki ba ya  cusa mana wata akida  ta daban ba. Kuma

    Hausawa kuna da tarihin zama Kuros Riba mai kyau domin ba a taba samun

    ku ko hannunku a wani yamutsi ba, mun gode da kuka shigo wajen taya

    mu tsaro da zaman lafiya”.

    Ita kuwa kallabi tsakanin rawuna a taron uwargida Immaculata Ekpenyong,wadda take kula  da  horar da matasa a ma’aikatar,  da ta mike bayan ta yi wa al’ummar arewar da shugabannin kwamitin godiya, matukar farin ciki ta nuna na ganin “ko da muka shigo zauren taron nan hankalina ya fi karkata kan matasa na kuma gan su

    wannan ya dada tabbatar mana cewa kun rungumi matasa ba za ku taba bari

    su yi zaman banza ko zama bata gari ba.  Ta ce “nan gaba gwamnati a shirye

    take idan za ta yi wa matasan jihar wata bita ko horo na koyar da sana’o’i,

    ma’aikatarmu za mu rubuto wa  wannan kwamiti ya ba mu matasa da za mu

    hada su da namu a horas da su ko a koya musu sana’a”.

    Sai dai kuma Immaculata, ta shawarci kwamitin da ya  shigar da ’yan asalin jihar

    da ke zaune cakude da ‘yan arewa a unguwar tasu kuma da a guji daukar

    doka a hannu da zarar wata matsala ta samu ku rika sanar wa ofishin nasu .

    Bayan da mataimakiyar ta gama jawabinta cikin farin ciki tare da

    murna ta bayar da dama ko idan akwai wani mai neman karin bayani ko

    tambaya, nan take kuwa Alhaji Sani Baba Gombe sarkin Nasarawa/Bacoco

    gari na ‘yan arewa tsantsa da ke karamar hukumar birnin Kalaba ya

    tambayi kwamishiniyar cewa “mu da aka haife mu a Kuros Riba, mu ma muka

    haifa ko mene ne ya sa ba a ba mu satifiket na zama dan kasa wato

    indigene certificate da kuma rika daukarmu aikin gwamnati a mataki na

    jiha, tun da nan muka yi karatu akwai mu, yaranmu da suka gama manyan

    makarantu da kuma jami’o’i “?.

    Immaculata Ekpenyong, ta bai wa Alhaji Baba Gombe da amsa da cewa,  “dan

    uwana magana ta gaskiya mu a nan Kuros Riba ba za mu iya daukar muku

    alkawari ba na  rika dukar ku aiki ba a matakina gwamnatin jiha, na san

    ana tafiya da ‘yan arewa a gwamantin jiha ana nada maku shugaban

    hukumar alhazai da kuma ba ku damar nada sarakunanku, kana kuma a

    wannan gwamnati, an nada muku mai ba Gwamna shawara kan bakin da ba ‘yan

    asalin jiha ba (na musamman), shawarar da zan ba ku a nan ita ce ku rika

    nema musu ta fuskar tarayya idan an kawo wani babban ma’aikaci na

    tarayya, ku rika mika musu bukatunku, za su taimaka, hanya mafi sauki ke

    nan .,

    Game da batun katin shaidar zama dan asalin jihar kuwa cewa ta yi

    “ A gaskiya wannan matsala ruwan dare ce a Nijeriya, akwai dan uwana

    mazaunin Kano ne can ma ya hayayyafa idan wani abu ya taso na karatun

    ‘ya’yansa shi ma gida Kuros Riba yake dawowa yana musu, ba zan yi karya

    ba domin a so ni”.injita.

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here