KWAMISHINAN LAFIYA A JIHAR YOBE YA TABBATAR DA RAHOTON MUTANE 10 SUN KAMU DA CUTAR SANKARAU

0
668
Gwamna Gaidam: Sha yabo katafila sarkin aiki

Muhammad Sani Chinade, DAGA DAMATURU

KWAMISHINAN ma\’aikatar lafiya a Jihar Yobe Alh Bello Kawuwa ya

tabbatar da cewar an samu mutane 10 da ke dauke da cutar nan ta

sankarau a cikin jihar kuma, 3 daga cikinsu tunin sun riga mu gidan

gaskiya.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a yayin da yake kaddamar gangamin

allurar riga-kafin cututtukan nan na kyanda da sankarau da ke yaduwa a

cikin al\’umma musamman a lokacin zafi da aka gudanar a garin Damaturu.

Ya kara da cewar, gwamnatin Jihar da hadin gwiwar hukumar samr da

harkokin kiwon lafiya a matakin farko ta kasa

(PHC).

Kwamishinan ya ci gaba da cewar, wannan riga-kafin da ake kokarin a kai za

a gudanar da shi ne a cibiyoyin kiwon lafiyar da aka tanada, ana kuma

kyautata zaton za a yi wa yara kimanin 771,778 riga-kafin.

Ya kara da cewar wannan aiki na riga-kafin za a gudanar da shi ne

bangare biyu na farko tunin aka fara gudanar da shi daga ranar 7 ga

watan nan na Fabrairu 2018 aka kare shi a ranar Lahdi 11 ga wata a

kananan hukumomi 8 sai kashi na biyu a gudanar da shi daga ranar 14 ga

watan na Fabrairu zuwa 18 ga watan.

Don haka ne kwamishinan ya nemi iyaye da su bada \’ya\’yansu don yi musu

wannan riga-kafi don hakkinmu ne mu iyaye da mu ga mun samarwa da

yaranmu yanayin lafiya mai nagarta.

 

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here