Mustapha Imrana Abdullahi Daga Kaduna
BAYANAI daga karamar hukumar Birnin Gwarin Jihar Kaduna na cewa a halin yanzu yawan mutanen da aka kashe sun Kai Saba\’in da Daya.
Kamar dai yadda Alkalumma suka Fara nunawa yawan wadanda suka rasa rayukan nasu na kara karuwa ne a kullum saboda irin yadda daruruwan mutane suka shiga cikin dajin inda kauyen Gwaska yake suna neman jama\’ar da suka tsere domin tsira da rayuwarsu.
Kamar dai yadda rahotanni suka bayyana daga kauyen Gwaska Sun ce an yi wa jama\’a kisan Gilla ne saboda sun ki amincewa su rika mu\’amala da masu satar shanu tun farko, \”mu\’amalar dai za ta iya kasancewa ta shiga a rika satar shanun ne da su ko Kuma su rika bada bayanai kamar yadda ake samun masu ba batagarin labarin yadda wasu abubuwa ke tafiya kafin su aiwatar da ayyukan masu\”.
Koda yake a jiya ne wasu Kafafen yada labarai masu cin gajeren zango a cikin Kaduna suka rika bayar da labarin Gwamna Nasiru El-Rufa\’i ya Kai ziyarar jaje garin Gwaska, kuma har ya Kai irin wannan ziyarar ga mai martaba Sarkin Birnin Gwari Bawan Allah Alhaji Zubairu Jibril Mai Gwari na ll