WANI MATASHI YA HAU HUSUMIYAR MASALLACI BAYAN YAYI ZINDIR

0
1004
Matashin da ya hau hasumiyyar masallaci
Daga Usman Nasidi

WANI matashi da ba a bayyana sunan a ba ya haye kan kololuwar hasumiyar masallacin juma’a na unguwar Ja’en da ke kan titin Sharada a garin Kano.

Matashin ya yi zigidir haihuwar uwarsa bayan ya haye bisa hasumiyar. Ya tube kayansa ya jefo su kasa.

Maigadin masallacin, Mallam Adda’u, ya bayyana cewar matashin ya karya wata taga ne kafin ya samu damar shiga masallacin kuma duk da sun yi kokarin dakatar da matashin hakan ba ta yiwu ba.

Sannan ya kara da cewa, matashin ya ce ba zai sauko ba saboda wasu na neman shi za su kashe shi, duk da bai bayyana ko su wane ne  ba.

Wani daga cikin ‘yan kwamitin masallacin, Malam Kabiru, ya ce sun sanar da jami’an ‘yan sanda bayan samun matashin cikin hasumiyar.

Daga bisani jami’an ‘yan sanda sun yi nasarar sauko da matashin tare da tafiya da shi ofishinsu domin zurfafa bincike a kansa.

Kwanakin baya wani matashi ya taba haye kan kololuwar karfen gidan Radiyon Kano da ke unguwar Tukuntawa tare da yin ikirarin cewar ba zai sauko ba sai an samar wa da matasa abin yi. Shi ma da kyar jami’an tsaro suka samu nasarar saukowa da shi daga karfen.

Bisa ga dukkan alamu matasan jihar Kano sun samo wani sabon salon hayewa kan gini ko karafa masu tsayi duk lokacin da suke da bukatar nuna fushi ko damuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here