SHAN MIYAGUN KWAYOYI NE KE KAWO AYYUKAN TA’ADDANCI A KASAR NAN- Inji BABA OTU

0
718

Isah Ahmed, Jos

SHUGABAN kungiyar tabbatar da adalci  da tsaro da tattaunawa tsakanin al’ummomin da suke rikici [JSDC ]da ke garin Jos babban birnin jihar Filato, Alhaji Lawal Baba Otu ya bayyana cewa shaye shayen miyagun kwayoyi da matasan kasar nan, suke yi ne yake kawo ayyukan ta’addancin da ake fama da su a kasar nan. Alhaji Lawal Baba Otu ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da wakilinmu.

Ya ce matsalar shaye shayen miyagun kwayoyi, matsala ce da take   damun al’ummar  kasa gabaki daya. Kuma mafiyawaci matasa ne suke shaye shayen wadannan miyagun kwayoyi.

Ya ce  idan aka cigaba da barin matasan kasar nan  suna shaye shayen miyagun qwayoyi, ba zasu amfani kansu ba, kuma ba zasu amfani kasa gabaki daya ba.

Alhaji Baba Otu ya yi bayanin cewa miyagun  kwayoyin nan a cikinmu ake sayar da su. Domin   a kowace unguwa akwai masu sayar da irin wadannan miyagun kwayoyi, ta hanyar fakewa da shagunan sayar da magunguna.

Ya ce a  wadannan  shagunan sayar da magunguna da suke unguwanninmu, a wajensu ake samun irin wadannan miyagun kwayoyi.

Alhaji Baba Otu  ya ce ganin irin illolin da shaye shayen miyagun kwayoyi, ya sanya kungiyarsu ta tashi tsaye wajen wayar kan jama’a kan illolin shaye shayen miyagun kwayoyi a garin Jos da kewaye.

‘’A wannan garin na Jos  mun ziyarci makarantun sakandire  na GSS West Of mine da GSS Unguwar rogo da GSS Gwom, mun wayar wa da dalibai kai, kan illolin shaye shayen miyagun kwayoyi. Haka kuma mun ziyarci unguwannin da dama da wuraren da matasa suke zama  a wannan gari, mun wayar masu da kai kan illolin shan miyagun kwayoyi’’.

Alhaji Baba Otu ya yaba wa gwamnatin jihar Filato kan kokarin da ta yi wajen ganin an sami zaman lafiya a jihar. Ya ce babu shakka gwamnan jihar Filato ya yi kokari wajen samar da zaman lafiya a jihar Filato.

Ya ce amma a hana  shigo da miyagun kwayoyi a jihar, shi ne zai  kawo  tabbatatcen zaman lafiya da bunkasar arziki a jihar.

Ya yi  kira ga al’ummar Nijeriya kan kowa ya tashi ya bada gudunmarsa, wajen  yaki da shan miyagun kwayoyi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here