MUTANEN AREWA BA SU TABA ROKON BUHARI YA YI MASU AYYUKAN RAYA KASA BA-SALE BAYARI

0
661
Alhaji Sale Bayare

Isah Ahmed, Jos

Shugaban kungiyar ci gaban al’ummar Fulani makiyaya ta Nijeriya ta Gan Allah Alhaji Sale Bayari, ya bayyana cewa shi bai taba ganin  inda mutanen Arewa suka zauna da shugaban kasa Muhammad Buhari,  suka  roki  ya yi masu  wasu ayyukan raya kasa kamar hanyoyi mota ko asibitoci  ba. Alhaji Sale Bayari ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron karramar da kungiyar daliban manyan makarantun arewa suka yi masa da Garkuwan matasan Arewa,   a garin Jos babban birnin jihar Filato a karshen makon da ya gabata.

Ya ce a  kullum mutanen yankin  Neja Delta suna cewa a yi masu kaza, a yi masu kaza kuma su ce  idan  ba a yi masu ba, ba za a dauki mai ba.

Ya ce amma mu mutanen Arewa ba mu taba cewa idan ba a yi mana kaza ba, ba za a dauki masara da tumatur da shanu daga Arewa a kai kudu ba.

‘’A yankin Neja Delta akwai mutanen da basa aikin komai, amma  in wata ya kare ana baiwa kowa Naira dubu 65. Yanzu a arewa muna da miliyoyin mutane da suke son a dauke su aikin da za a rika basu naira dubu 18, a wata.  Yanzu idan ka je Ibadan za  ka ga hanyar mota da ake yi. Kaje Asaba ka ga gadar da ake yi. Ana yi masu irin wadannan ayyuka ne saboda suna nema a yi masu’’.

Alhaji Sale Bayari ya ce ya kamata mutanen Arewa su rika fitowa suna mika bukatun abubuwan da suke son a yi masu. Shima shugaban Buhari  ya kamata  ya san cewa mutanen arewa suna sonsa, ta hanyar yi masu  wasu abubuwa na ci gaba.

Alhaji Sale Bayari ya ce yaji  mamaki da wannan kungiya suka san shi kuma suka  san abubuwan da yake yi, har suka karrama shi da  Garkuwan matasan Arewa. Don haka ya ce babu abin da zai ce kan wannan karramawa da aka yi masa, sai dai ya ce ya gode.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here