Mawakan  Siyasa Sune Gishirin Dimokuradiyya Na Moroko.

    0
    928

     

    JABIRU A HASSAN, Daga Kano.

    AN bayyana cewa  mawakan siyasa sune gishirin dimokuradiyya idan aka dubi irin gagarumar gudummawar da suke baiwa harkokin siyasa tare da kasancewa masu  aika sakonni  na gyara kayanka ga al\’umar da ake yiwa  shugabanci ko kuma shugabanni.

    Wannan tsokaci ya fito ne daga fitaccen mawakin siyasar nan dàke jihar kano, Malam Sulaiman Leri Dawakin Tofa  wanda akafi sani dà Sule nà Maroko a wata hirà da sukà yi da wakilin mu, inda ya ssnar da cewa ko shakka babu, mawakan siyasa sune suke fadakar  da al\’ uma irin muhimman abubuwan dà kasa ke ciki ko kuma sahihancin mutanen da suke neman a zabe su kan mukamai dabàn-dabàn.

    Haka kuma Malam Suleimàn na Maroko yace a tsari irin na dimokuradiyya, mawakan siyasa sune suke nuna amfànin mutane dake bukatar tàkara a jàm\’iyyu daban-daban ta yadda kowa zai duba nagartar wanda yàke so yà shugaban ce shi, tare da yin kira gà yàn uwansa mawakan siyasa da su rika mutunta mutanen da suke wasawa ko abokàn hamayyàr su domin ganin ana yin adawa mài amfàni.

    Mawakin siyasar ya yi amfàni da wannan dama wajen yin fatàn alheri  ga dukkanin mawakan siyasar dake kasarnan bisa yadda aka hadu ana aikin bunkasa dimokuradiyya, sannan yayi godiyà ta musamman ga iyayen gidàn sa na siyasa da masu neman madafar iko a matàkai dàbàn-daban dàke fadin kasarnan.

    Daga karshe, Malam Sulaiman Leri na Maroko ya sanar dà cewa zai fitar dà wasu sabbin wakoki  kan  siyasar Nijeriya dà shirin zabukan 2019 da yaddà al\’uma zasu fàhimci alkiblàr ciyàr dà kasa gàba, inda kuma ya nunar da cewa dukkanin masu bukatar samun wakokin sa ko wani karin bayani sai a tuntube shi akan lambar sa ta waya 08065307878

    LEAVE A REPLY

    Please enter your comment!
    Please enter your name here