Gwamna Ganduje Ya Hana Bara Domin Tsaftace Neman Ilimin Addini Da Na Zamani

0
423
  •  

    Jabiru A Hassan, Daga Kano.
    
    An bayyana cewa hana  barace-barace kan tituna barkatai  da gwamnatin jihar kano ta sanar zai kawo tsafta wajen neman  ilimin addini dana  zamani musamman yadda gwamna Dokta Abdullahi Umar Ganduje yake  daukar matakai na bunkasa ilimi a jihar  tareda kyautata tarbiyya ta shirin bada  ilimi kyauta kuma dole a jihar  kano.
    
    Wannan bayani ya fito ne  daga  wasu  malamai daga  yankunan karkara da  suka  zantawa da Gaskiya Tafi Kwabo inda suka nunar da  cewa ko  shakka babu, gwamna Ganduje ya daura damarar tsaftace neman  ilimin addinin  musulunci da kuma kawo tsari mai  gamsarwa ga yara ta yadda abin zai amfani al'uma ta kowane fanni.
    
    Malam Adamu Musa, malami mai  koyar da  karatun allo  ga dalubai fiye da  50, yace  mafiya yawan lokuta akan sami yara masu barace-barace cikin laifuka sannan wasun su ma basa  yin karatu kuma tuni sun bar malaman su na ainihi da  aka damka su garesu wanda  hakan ko  kadan ba daidai bane.
    
    Shi ma da  yake  nasa  bayanin, malam Muhammadu Saye  ya nunar da  cewa hana  barace-barace da  gwamnatin kano tayi ba abin tada hankali bane, domin  idan aka duba za'a fahinci cewa anyi  hakan ne  da  kyakykyawar niyya wajen kawo tsafta a sha'anin neman  ilimi da  tarbiyya kamar  yadda ake  gani a kasashen musulmi na duniya.
    
    Wani almajiri da  aka kai  Kano daga jihar  Katsina  mai suna lawwali Abubakarya shaidawa wakilin mu  cewa tun  da  aka kaishi kano bai yi karatu ba sai  dai bara da  neman  kudi da  zuwa gidajen mai  wanda  a cewarsa,hakan ta sanya  yake  ganin hana  bara da  gwamnatin jihar  tayi abu  ne  da  bai sabawa Shari'a ba.
    
    Sai  dai wani bincike da  Gaskiya  Tafi Kwabo ta yi ya nunar da  cewa mafiya yawan almajirai dake  barace-barace ana  kai  su makarantar allo ne  saboda iyayen su watau uwa da  uba basu tare kuma babu wanda  zai kula da  ire-iren wadannan yara illa a Kai su makarantun allo  batare da  yin la'akari da inda ake  kai su ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here