An Rusa Gidajen Sama 50 A Narkuta Da Ke Jos

0
559
Wani bangare na gidajen da aka rusa a Narkuta

Isah  Ahmed Daga Jos

AKALLA ma’aikata masu aikin rushe gini tare da kariyar jami’an tsaro daga jami’ar Jos, sun rushe gidaje sama da 50 a garin Narkuta da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa  a Jihar Filato, a ranar asabar din da ta gabata.

Idan ba a manta ba, makonni biyu da suka mun  buga labarin rikicin da ya faru a garin na Narguta, wanda ya yi sanadin rasa ran mutum daya, kan takaddamar mallakar fili da ake yi,  tsakanin jami’ar Jos da al’ummar garin Narguta.

Da yake zantawa da ‘yan jarida kan wannan al’amari,  a fadarsa da ke garin na Narkuta Sarkin na Narguta Injiniya Muhammad Bello ya bayyana takaicinsa kan faruwar wannan al’amari.

Ya ce  a safiyar ranar asabar da safe sai suka tashi suka  ga jami’an tsaro, sun kewayemu tare da ma’aikata daga jami’ar Jos da motocin rushe gini,  suka fitar da mutanensu daga gidajensu suka kama rushe gidajen.

Ya  ce a wannan abu da aka yi mana wanda aka take mana haqqinmu na dan adam, an rusa mana gidaje a kalla sama da guda 50.

‘’ A matsayinmu na masu son zaman lafiya da bin doka da oda muna bin dukkan hanyoyin da suka kamata, wajen ganin an warware wannan takaddama  kan mallakar wannan fili. Don haka muna kira ga masu ruwa da tsaki kan wannan al’amari, na ciki da wajen Jihar Filato su dubi wannan abu da aka yi mana, na rushe mana gidaje wanda ya jefa iyalanmu cikin mawuyacin hali, don warware wannan takaddama’’.

A lokacin da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na Jami’ar ta Jos, Mista Abdllahi Abdullahi don jin ta bakinsa kan wannan al’amari, ya bayyana cewa ba zai iya cewa komai ba, domin yanzu yana hutu ne.

Jami’ar ta Jos da al’ummar garin na Narkuta dukkansu kowa yana ikirarin cewa shi ne ya mallaki wannan fili da ake takaddama, wanda al’ummar garin na Narkuta suka yi gine gine a ciki.

A wata sanarwa da al’ummar na garin na  Narakuta suka fitar, sun bayyana cewa  sun sayi wannan fili ne, daga kamfanin Ron Properties Nig LTD  a madadin Iyalan Wakili Jatau da suka bashi hakkin sayar da filin, da sune asalin suke da mallakarsa.

A yayinda itama a wata  sanarwar da ta fitar da ke dauke da sanya hanun mataimakin babban magatakardar Jami’ar ta Jos, Wilson Yale  ta bayyana cewa Jami’ar ta Jos  ta sayi wannan fili ne daga kamfanin yin jan bulo na  Nigeria Bricks and Clay Product  LTD ta hanun kamfanin sayar da kadarorin gwamnati na BPE

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here