An Dakatar Da ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Kano 5 Zuwa Wata 6

0
541
Rabo Haladu Daga Kaduna
MAJALISAR dokokin jihar Kano ta dakatar da ‘ya’yanta biyar zuwa wata shida bayan an zarge su da  keta dokokin majalisar.
Shugaban majalisar, Abdulazeez Gafasa ne ya sanar da dakatar da Garba Ya’u Gwarmai da Labaran Audu Madari da Isyaku Ali Danja da Bello Muhammad da kuma Salisu Ahmad Gwangwazo
Ya ce sun dauki matakin ne saboda yunkurin da ‘yan majalisar suka yi na dauke sandar majalisar a makon jiya.
‘Yan majalisar dai sun yi yunkurin dauke sandar ne saboda zargin da suka yi cewa gwamnatin Abdullahi Ganduje ta hada baki da wasu ‘yan majalisar domin yin amfani da majalisar wurin sauke Sarki Muhammadu Sanusi na II.
Manema labarai sunyi yunkurin jin ta bakin dukkan bangarorin amma bata abin yacitura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here