An Zabi Sababbin Shugabannin Kungiyar Ma’aikatan Karamar Hukumar Lere

1
837
Jamilu Sani sabon shugaban kungiyar ma'aikatan Karamar Hukumar Lere

Isah Ahmed Daga Jos

MA’AIKATAN Karamar Hukumar Lere da ke Jihar Kaduna, sun zabi sababbin shugabannin kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi ta Najeriya [NULGE] reshen Karamar hukumar. Ma’aikatan sun gudanar da zaben sababbin shugabannin  nasu ne, a sakatariyar Karamar hukumar da ke garin Saminaka.

Sababbin shugabannin da aka zaba, sun hada da Jamilu Sani a matsayin shugaba, da  Bako Kawu mataimakin  shugaba  da Ahmed Abdullahi Sakatare,  da  Stephen Garba mataimakin Sakatare  da Abdul Munka’ila Ma’ajiyi, da Aqilu Yarima Dattijon qungiya da Serah Ishaya shugabar mata.

Sauran sune  Nura Abdullahi mai binciken kuxi  da Hamisu Ibrahim wakilin sashin  harkokin mulki da kuxi, da Usman Yet wakilin sashin ayyuka  da Sama’ila Ahmed Wakilin sashin noma  da Salmanu Umar wakilin  sashin ilmi da walwala, da kuma Ibrahim Jamilu Abubakar  shugaban matasa  na ma’aikatan.

Da yake jawabi a wajen Daraktan ma’aikata na Karamar hukumar Lere, Alhaji Adamu Gubuci ya bayyana matukar farin cikinsa kan yadda aka gudanar da wannan zabe lafiya.

Ya yi  kira ga sababbin shugabannin  da aka zaba su yi adalci, kan wannan zabe da aka yi masu.

Ya yi addu’a ga shugabannin kan  Allah ya taimakesu kan wannan aiki da aka dora masu, kuma  ya sanya  su gama lafiya.

A nasa jawabin Shugaban kungiya ma’aikatan kananan hukumomi ta Najeriya [NULGE] reshen Jihar  Kaduna Kwamared Rayyanu Isiyaku Turunku ya bayyana cewa babu shakka ma’aikatan karamar hukumar Lere, sun zabi shugabannin da suke so. Don haka ya yi fatar  shugabanni za su tallafa wa ma’aikatan wannan karamar hukuma.

Shugaban ma’aikatan, wanda shugaban kungiyar ma’aikatan Karamar Hukumar Birnin Gwari,  Kwamaren Shu’aibu Jibrin ya wakilta, ya   yi  kira ga ma’aikatan   su rika zuwa aiki  kan lokaci kuma su rika zama a wurin aiki, har zuwa lokacin tashi.

Ya yi  kira ga  ma’aikatan kananan hukumomi na jihar Kaduna, su ci gaba da kasancewa masu biyayya kamar yadda  da aka san su.

A nasa jawabin a madadin wadanda aka zaba sabon shugaban kungiyar Jamilu Sani ya mika  godiyarsu  ga Allah, da dukkan  ma’aikatan wannan karamar hukuma, kan wannan zabe da aka yi masu.

Ya ce babu shakka wannan wata  rana ce mai matukar tarihi a gare mu, saboda jama’a sun fito sun zabi shugabannin da suke bukata.

Ya ce saboda kyakyawan zaton da ake yi masu ya sa aka zabe su, don haka da yardar  Allah za su ba marada kunya, wajen ganin sun gudanar da ayyukan su tsakani da Allah.

Ya yi kira ga ma’aikatan su ci gaba da ba su goyan baya da hadin kai kuma su ci gaba da yi masu addu’a.

1 COMMENT

  1. Hakika mai katan karamar hukumar lere yanzune suka zabi shuwagaban nin ma aikata masu son cigaban karamar hukumar Allah ya tayaku riko jamilu sani Ang mela

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here